• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Dokar Bai Wa Auren Jinsi Kariya: Gwamnatin Tarayya Ta Koka Kan Rahoton Wata Jarida

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Zargin Dokar Bai Wa Auren Jinsi Kariya: Gwamnatin Tarayya Ta Koka Kan Rahoton Wata Jarida
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta koka kan yadda wata jarida wacce ba LEADERSHIP ba ke rahoto abinda ta kira da “rahotannin ƙarya”.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana haka a wani taro da ya yi da manema labarai a Cibiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa da ke Abuja a ranar Asabar.

  • Kasar Ingila Ta Tsallaka Zuwa Matakin Semi Final A Gasar EURO Ta 2024
  • ‘Yan Fashin Daji Sun Sace Wasu ‘Yan Jarida Da Mata Da Wasu Yara 2 A Kaduna

Ya yi jawabi ne sakamakon hayaniyar da ta tashi bayan jaridar ta buga labari cewa, gwamnatin Nijeriya ta rattaba hannu a ƙasar Samoa kan wata yarjejeniya da za ta ba ‘yan luwaɗi da masu maɗigo cikakken ‘yanci a ƙasar nan (Nijeriya).

Labarin ya harzuka jama’a tare da haifar da suka kan gwamnatin Tinubu.

A taron, Minista Idris ya ce gwamnati mai ci yanzu tana mutunta ‘yancin faɗin albarkacin baki da suka mai ma’ana to amma ta damu da “rahotannin ƙarya” da ke fitowa daga jaridar.

Labarai Masu Nasaba

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

Ya ce: “Gwamnatin Tarayya, a ƙarƙashin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, gwamnati ce mai kyautata alaƙa da kafafen yaɗa labarai. Hakan ya yi daidai da aƙidar Shugaban Ƙasa a matsayinsa na wanda ya daɗe yana gwagwarmayar tabbatar da dimokuraɗiyya da ‘yancin ɗan Adam.”

Alhaji Idris ya yi nuni da cewa, gwamnati ta ba kafafen yaɗa labarai damar su yi suka da kuma kare ‘yancin faɗin albarkacin baki ga jama’a.

Ya ce, “Amma abin baƙin ciki ne yadda wasu mutane suke wasa da wannan kyakkyawan yanayin wanda gwamnati ta tanadar. Mun yi matuƙar mamakin yawan aikin jarida da kuma kalamai na ganganci da wasu gidajen watsa labarai da mutane suke yi waɗanda suna da illa ga tsaron ƙasa.

“A ganinmu, wannan abin kunya da rashin imani ne domin kuwa babu wannan zancen a cikin takardun da aka sanya wa hannu.

“Abin mamaki, jaridar ba ta ba da wata shaida ba ko ta kawo yarjejeniyar da ta ce an rattaba wa hannu domin kafa hujja.

“Abin baƙin ciki ne a ce labarin maras tushe kuma mai tayar da hankali shi ne wasu limamai suka yi amfani da shi a huɗubarsu bayan an yaudare su da labarin, wanda hakan ya ƙara tunzura jama’a.”

Idris ya ce duk da waɗannan al’amurran, gwamnati za ta bi doka kuma ba za ta ɗauki tsauraran matakai ba.

Ya ce: “Gwamnatocin da suka shuɗe sun rufe gidajen kafafen yaɗa labarai kan abubuwan da ba su kai wannan muni ba, amma mu za mu bi abin a hankali kuma bisa doka.”

Idris ya bayyana cewa gwamnati za ta kai maganar ga Ƙungiyar Mamallaka Gidajen Jaridu ta Nijeriya (NPAN) tare da shigar da ƙara.

Ya ce: “Gwamnatin Tarayya tana goyon bayan kafafen yaɗa labarai masu ɗa’a da faɗin albarkacin baki amma ba za ta amince da labaran ƙarya da ke cutar da zaman lafiya da tsaron ƙasa ba.”

Idris ya halarci taron manema labaran ne tare da Ministan Kasafin Kuɗi Da Tsare-tsaren Ƙasa wanda ya yi ƙarin haske kan yarjejeniyar ta Samoa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Auren JinsiLuwadiMadigoYarjejeniyar Samoa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilan Da Yasa Ba’a Gani Na Cikin Tawagar ‘Super Eagles’ A Halin Yanzu -Ahmed Musa

Next Post

Cika Shekaru 161: Rundunar Sojojin Nijeriya Ta Tallafawa Marayu 400 A Zamfara

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

29 minutes ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

1 hour ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

2 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

4 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

6 hours ago
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta
Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

10 hours ago
Next Post
Cika Shekaru 161: Rundunar Sojojin Nijeriya Ta Tallafawa Marayu 400 A Zamfara

Cika Shekaru 161: Rundunar Sojojin Nijeriya Ta Tallafawa Marayu 400 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.