ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Dokar Bai Wa Auren Jinsi Kariya: Gwamnatin Tarayya Ta Koka Kan Rahoton Wata Jarida

by Sulaiman
2 years ago
Auren jinsi

Gwamnatin Tarayya ta koka kan yadda wata jarida wacce ba LEADERSHIP ba ke rahoto abinda ta kira da “rahotannin ƙarya”.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana haka a wani taro da ya yi da manema labarai a Cibiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa da ke Abuja a ranar Asabar.

  • Kasar Ingila Ta Tsallaka Zuwa Matakin Semi Final A Gasar EURO Ta 2024
  • ‘Yan Fashin Daji Sun Sace Wasu ‘Yan Jarida Da Mata Da Wasu Yara 2 A Kaduna

Ya yi jawabi ne sakamakon hayaniyar da ta tashi bayan jaridar ta buga labari cewa, gwamnatin Nijeriya ta rattaba hannu a ƙasar Samoa kan wata yarjejeniya da za ta ba ‘yan luwaɗi da masu maɗigo cikakken ‘yanci a ƙasar nan (Nijeriya).

ADVERTISEMENT

Labarin ya harzuka jama’a tare da haifar da suka kan gwamnatin Tinubu.

A taron, Minista Idris ya ce gwamnati mai ci yanzu tana mutunta ‘yancin faɗin albarkacin baki da suka mai ma’ana to amma ta damu da “rahotannin ƙarya” da ke fitowa daga jaridar.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Ya ce: “Gwamnatin Tarayya, a ƙarƙashin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, gwamnati ce mai kyautata alaƙa da kafafen yaɗa labarai. Hakan ya yi daidai da aƙidar Shugaban Ƙasa a matsayinsa na wanda ya daɗe yana gwagwarmayar tabbatar da dimokuraɗiyya da ‘yancin ɗan Adam.”

Alhaji Idris ya yi nuni da cewa, gwamnati ta ba kafafen yaɗa labarai damar su yi suka da kuma kare ‘yancin faɗin albarkacin baki ga jama’a.

Ya ce, “Amma abin baƙin ciki ne yadda wasu mutane suke wasa da wannan kyakkyawan yanayin wanda gwamnati ta tanadar. Mun yi matuƙar mamakin yawan aikin jarida da kuma kalamai na ganganci da wasu gidajen watsa labarai da mutane suke yi waɗanda suna da illa ga tsaron ƙasa.

“A ganinmu, wannan abin kunya da rashin imani ne domin kuwa babu wannan zancen a cikin takardun da aka sanya wa hannu.

“Abin mamaki, jaridar ba ta ba da wata shaida ba ko ta kawo yarjejeniyar da ta ce an rattaba wa hannu domin kafa hujja.

“Abin baƙin ciki ne a ce labarin maras tushe kuma mai tayar da hankali shi ne wasu limamai suka yi amfani da shi a huɗubarsu bayan an yaudare su da labarin, wanda hakan ya ƙara tunzura jama’a.”

Idris ya ce duk da waɗannan al’amurran, gwamnati za ta bi doka kuma ba za ta ɗauki tsauraran matakai ba.

Ya ce: “Gwamnatocin da suka shuɗe sun rufe gidajen kafafen yaɗa labarai kan abubuwan da ba su kai wannan muni ba, amma mu za mu bi abin a hankali kuma bisa doka.”

Idris ya bayyana cewa gwamnati za ta kai maganar ga Ƙungiyar Mamallaka Gidajen Jaridu ta Nijeriya (NPAN) tare da shigar da ƙara.

Ya ce: “Gwamnatin Tarayya tana goyon bayan kafafen yaɗa labarai masu ɗa’a da faɗin albarkacin baki amma ba za ta amince da labaran ƙarya da ke cutar da zaman lafiya da tsaron ƙasa ba.”

Idris ya halarci taron manema labaran ne tare da Ministan Kasafin Kuɗi Da Tsare-tsaren Ƙasa wanda ya yi ƙarin haske kan yarjejeniyar ta Samoa.

Auren jinsi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Cika Shekaru 161: Rundunar Sojojin Nijeriya Ta Tallafawa Marayu 400 A Zamfara

Cika Shekaru 161: Rundunar Sojojin Nijeriya Ta Tallafawa Marayu 400 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.