• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ZARGIN MAITA: Mahaukaciya Ta Razana Al’umma A Kaduna

by Shehu Yahaya
2 years ago
in Al'ajabi, Manyan Labarai
0
ZARGIN MAITA: Mahaukaciya Ta Razana Al’umma A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar Unguwar Mangwaron Agwai da Malalin Gabas da ke cikin karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna, sun fada cikin rudani kan bayyanar wata mata da suke zargin mayya ce.

Al’ummar wadanda tuni suka fara tserawa suna barin gidajensu domin neman mafaka a unguwanni makwabta.

  • ‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 4 Tare Da Cafke 9 A Jihar Kaduna.
  • Yadda Bullar Cutar Gansakuka Ta Sa Manoman Citta Tafka Mummunar Asara A Kaduna

lamarin ya faru ne ranar litinin 11 ga watan Satumbar 2023 da misalin karfe 2 na rana, ganin yadda matan suka fito tsirara babu kaya a jikinsu suna yawo layi-layi suna sumbatu lamarin da haifar da tsoro da fargaba a unguwar, musamma mata da matasa.

Ganin Hakan ya sanya wasu fusatattu suka kama wata mata mai shekaru kusan 55 suka lakada mata dukan kawo wuka, wacce da kyar jami’an tsaron sai kai na JTF suka kwace ta.

Da farko dai matar ta tsorata kowa hatta jami’an tsaron na JTF sun fara gudu daga ofishin nasu sai daga bisani da suka fahimci cewa matar kamar tana da tabin hankali, hasalima, idan suka bar matasa da matar suna iya daukar doka a hannunsu na yin kisa.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Lokacin da wakilinmu ya shiga unguwar ya yi kicibis da mata da yara suna gudu suna addu’oin neman kariya daga Allah, lamarin da ya kai matan aure suna ta rufe gidanjensu suna barin gida. Wasu mata da wakilinmu ya ci karo da su ya ga suna gudu suna kiran ” mun shiga uku mayu sun shigo mana gari! Ga su can mayu ne su biyu !! .

Binciken da wakilinmu ya gudanar ya nuna cewa matar tana fama da tabin hankali ne ba maita ba, musamman ganin yadda ‘Yan JTF suka rinka yi wa matar tambayoyi.

A zantawarsa da wakilinmu Sakataren JTF na gundumar Mangwaron Agwai Mohammed Suleiman, ya ce “wasu matasa ne suka lakada wa matar duka bisa zargin ita mayya ce saboda sun ganta tana yawo tsirara babu kaya a jikinta hakan ya sanya mu kuma muka kwace ta a hannunsu”

Ya bayyana cewa “Mun fara samun bayanin ne tun da safiyar litinin din nan cewa wasu mata da ake zargin mayu ne sun bayyana a unguwar Mangwaron Agwai sai muka fara bincike a kai zuwa da rana kamar karfe 2, sai muka ga mutane suna ta guje-guje wai mayu sun bayyana a a unguwarmu kamun kace kwabo har wasu fusatattun matasa sun kama wata mata sun lakada mata duka, sun yi mata jina-jina, nan da nan muka kwaci matar domin yi mata tambayoyi da gudanar da bincike akan lamarin”

Ya kara da cewa ” Bayan mun kammala bincikenmu akanta sai muka fahimci cewa matar tana da tabin hankali wanda tuni muka mikata wurin ‘Yansanda a Rafin Guza, inda nan ma suka tabbatar mana da cewa matar tana da tabin hankali kuma zuwa gobe akwai yiwuwar su sake ta” inji shi.

Unguwar Mangwaron Agwai da Malalin Gabas sun yi kaurin suna wajen samun yawaitar mayu da matsalar rashin tsaro, hakan ya sanya matan aure da yara kanana suke zaman dar-dar a yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaZargin Maita
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadarin Mota Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum 2 A Kan Hanyar Legas Zuwa Abeokuta

Next Post

Paul Pogba Na Fuskantar Dakatarwa Bayan Samunsa Da Laifin Shan Kwayoyi

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

7 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

23 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Paul Pogba Na Fuskantar Dakatarwa Bayan Samunsa Da Laifin Shan Kwayoyi

Paul Pogba Na Fuskantar Dakatarwa Bayan Samunsa Da Laifin Shan Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Kaduna

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.