• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ZARGIN MAITA: Mahaukaciya Ta Razana Al’umma A Kaduna

by Shehu Yahaya
2 years ago
in Al'ajabi, Manyan Labarai
0
ZARGIN MAITA: Mahaukaciya Ta Razana Al’umma A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar Unguwar Mangwaron Agwai da Malalin Gabas da ke cikin karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna, sun fada cikin rudani kan bayyanar wata mata da suke zargin mayya ce.

Al’ummar wadanda tuni suka fara tserawa suna barin gidajensu domin neman mafaka a unguwanni makwabta.

  • ‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 4 Tare Da Cafke 9 A Jihar Kaduna.
  • Yadda Bullar Cutar Gansakuka Ta Sa Manoman Citta Tafka Mummunar Asara A Kaduna

lamarin ya faru ne ranar litinin 11 ga watan Satumbar 2023 da misalin karfe 2 na rana, ganin yadda matan suka fito tsirara babu kaya a jikinsu suna yawo layi-layi suna sumbatu lamarin da haifar da tsoro da fargaba a unguwar, musamma mata da matasa.

Ganin Hakan ya sanya wasu fusatattu suka kama wata mata mai shekaru kusan 55 suka lakada mata dukan kawo wuka, wacce da kyar jami’an tsaron sai kai na JTF suka kwace ta.

Da farko dai matar ta tsorata kowa hatta jami’an tsaron na JTF sun fara gudu daga ofishin nasu sai daga bisani da suka fahimci cewa matar kamar tana da tabin hankali, hasalima, idan suka bar matasa da matar suna iya daukar doka a hannunsu na yin kisa.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Lokacin da wakilinmu ya shiga unguwar ya yi kicibis da mata da yara suna gudu suna addu’oin neman kariya daga Allah, lamarin da ya kai matan aure suna ta rufe gidanjensu suna barin gida. Wasu mata da wakilinmu ya ci karo da su ya ga suna gudu suna kiran ” mun shiga uku mayu sun shigo mana gari! Ga su can mayu ne su biyu !! .

Binciken da wakilinmu ya gudanar ya nuna cewa matar tana fama da tabin hankali ne ba maita ba, musamman ganin yadda ‘Yan JTF suka rinka yi wa matar tambayoyi.

A zantawarsa da wakilinmu Sakataren JTF na gundumar Mangwaron Agwai Mohammed Suleiman, ya ce “wasu matasa ne suka lakada wa matar duka bisa zargin ita mayya ce saboda sun ganta tana yawo tsirara babu kaya a jikinta hakan ya sanya mu kuma muka kwace ta a hannunsu”

Ya bayyana cewa “Mun fara samun bayanin ne tun da safiyar litinin din nan cewa wasu mata da ake zargin mayu ne sun bayyana a unguwar Mangwaron Agwai sai muka fara bincike a kai zuwa da rana kamar karfe 2, sai muka ga mutane suna ta guje-guje wai mayu sun bayyana a a unguwarmu kamun kace kwabo har wasu fusatattun matasa sun kama wata mata sun lakada mata duka, sun yi mata jina-jina, nan da nan muka kwaci matar domin yi mata tambayoyi da gudanar da bincike akan lamarin”

Ya kara da cewa ” Bayan mun kammala bincikenmu akanta sai muka fahimci cewa matar tana da tabin hankali wanda tuni muka mikata wurin ‘Yansanda a Rafin Guza, inda nan ma suka tabbatar mana da cewa matar tana da tabin hankali kuma zuwa gobe akwai yiwuwar su sake ta” inji shi.

Unguwar Mangwaron Agwai da Malalin Gabas sun yi kaurin suna wajen samun yawaitar mayu da matsalar rashin tsaro, hakan ya sanya matan aure da yara kanana suke zaman dar-dar a yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaZargin Maita
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadarin Mota Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum 2 A Kan Hanyar Legas Zuwa Abeokuta

Next Post

Paul Pogba Na Fuskantar Dakatarwa Bayan Samunsa Da Laifin Shan Kwayoyi

Related

An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

46 minutes ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

7 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

8 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

11 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

20 hours ago
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

22 hours ago
Next Post
Paul Pogba Na Fuskantar Dakatarwa Bayan Samunsa Da Laifin Shan Kwayoyi

Paul Pogba Na Fuskantar Dakatarwa Bayan Samunsa Da Laifin Shan Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.