ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ZARGIN MAITA: Mahaukaciya Ta Razana Al’umma A Kaduna

by Shehu Yahaya
3 years ago
Kaduna

Al’ummar Unguwar Mangwaron Agwai da Malalin Gabas da ke cikin karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna, sun fada cikin rudani kan bayyanar wata mata da suke zargin mayya ce.

Al’ummar wadanda tuni suka fara tserawa suna barin gidajensu domin neman mafaka a unguwanni makwabta.

  • ‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 4 Tare Da Cafke 9 A Jihar Kaduna.
  • Yadda Bullar Cutar Gansakuka Ta Sa Manoman Citta Tafka Mummunar Asara A Kaduna

lamarin ya faru ne ranar litinin 11 ga watan Satumbar 2023 da misalin karfe 2 na rana, ganin yadda matan suka fito tsirara babu kaya a jikinsu suna yawo layi-layi suna sumbatu lamarin da haifar da tsoro da fargaba a unguwar, musamma mata da matasa.

ADVERTISEMENT

Ganin Hakan ya sanya wasu fusatattu suka kama wata mata mai shekaru kusan 55 suka lakada mata dukan kawo wuka, wacce da kyar jami’an tsaron sai kai na JTF suka kwace ta.

Da farko dai matar ta tsorata kowa hatta jami’an tsaron na JTF sun fara gudu daga ofishin nasu sai daga bisani da suka fahimci cewa matar kamar tana da tabin hankali, hasalima, idan suka bar matasa da matar suna iya daukar doka a hannunsu na yin kisa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Lokacin da wakilinmu ya shiga unguwar ya yi kicibis da mata da yara suna gudu suna addu’oin neman kariya daga Allah, lamarin da ya kai matan aure suna ta rufe gidanjensu suna barin gida. Wasu mata da wakilinmu ya ci karo da su ya ga suna gudu suna kiran ” mun shiga uku mayu sun shigo mana gari! Ga su can mayu ne su biyu !! .

Binciken da wakilinmu ya gudanar ya nuna cewa matar tana fama da tabin hankali ne ba maita ba, musamman ganin yadda ‘Yan JTF suka rinka yi wa matar tambayoyi.

A zantawarsa da wakilinmu Sakataren JTF na gundumar Mangwaron Agwai Mohammed Suleiman, ya ce “wasu matasa ne suka lakada wa matar duka bisa zargin ita mayya ce saboda sun ganta tana yawo tsirara babu kaya a jikinta hakan ya sanya mu kuma muka kwace ta a hannunsu”

Ya bayyana cewa “Mun fara samun bayanin ne tun da safiyar litinin din nan cewa wasu mata da ake zargin mayu ne sun bayyana a unguwar Mangwaron Agwai sai muka fara bincike a kai zuwa da rana kamar karfe 2, sai muka ga mutane suna ta guje-guje wai mayu sun bayyana a a unguwarmu kamun kace kwabo har wasu fusatattun matasa sun kama wata mata sun lakada mata duka, sun yi mata jina-jina, nan da nan muka kwaci matar domin yi mata tambayoyi da gudanar da bincike akan lamarin”

Ya kara da cewa ” Bayan mun kammala bincikenmu akanta sai muka fahimci cewa matar tana da tabin hankali wanda tuni muka mikata wurin ‘Yansanda a Rafin Guza, inda nan ma suka tabbatar mana da cewa matar tana da tabin hankali kuma zuwa gobe akwai yiwuwar su sake ta” inji shi.

Unguwar Mangwaron Agwai da Malalin Gabas sun yi kaurin suna wajen samun yawaitar mayu da matsalar rashin tsaro, hakan ya sanya matan aure da yara kanana suke zaman dar-dar a yankin.

Kaduna
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Paul Pogba Na Fuskantar Dakatarwa Bayan Samunsa Da Laifin Shan Kwayoyi

Paul Pogba Na Fuskantar Dakatarwa Bayan Samunsa Da Laifin Shan Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.