• English
  • Business News
Saturday, May 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)

by Sulaiman and Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
3 years ago
in Dausayin Musulunci
0
Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An so idan akwai hali, mai ziyara ya yi kwana takwas a Madina yana gabatar da sallolin farillan nan guda biyar
tare da Annabi (SAW) a Masallacinsa. Ma’ana mutum yana sallah ga kuma Annabi (SAW) a Masallacin.

Idan kuma Hukumar Alhazai ba ta bari ba, shikenan. Ko na kwana daya mutum ya yi da Annabi (SAW) ya isa dukkan falala.

  • Ziyarar Kabarin Annabi (SAW) 1

Dole ne ko wane Musulmin Kwarai ya girmama Manzon Allah (SAW) ya daraja shi tare da bin sa.
A cikin Alkur’ani maigirma Allah (SWT) ya ce, &kuot;Mu muka aiko ka – ya Rasulallahi a matsayin – maishaida, maibishara, maigargadi (ga al’ummarka), – ku kuma al’ummarsa – ku yi imani da Allah, da Manzonsa, ku daraja shi, ku kai matukar girma wurin daraja shi.&kuot;
Malam Mubarridu ya ce ma’anar &kuot;wa tu’azziruhu&kuot; a cikin ayar ita ce &kuot;ku kai matuka cikin girmama Manzon Allah (SAW).

Don haka Musulmi kar su yarda wani ya rude su ya yi musu dodorido idan an ga suna girmama Annabi (SAW) a ce musu ‘yan bid’ah sai su ji shakka su daina. Da irin wannan fahimtar ce aka je aka tada wa Annabi (SAW) bom a Masallacinsa.

Hatta Sahabban Annabi (SAW) sun fuskanci irin haka, babu abin da ba a fada musu ba, an ce musu wawaye saboda sun yi imani kuma duk abin da Manzon Allah (SAW) ya ce su yi ba sai sun tambaya ba, kawai yi suke.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Malamai sun bayyana cewa girmama Manzon Allah (SAW) bayan rasuwarsa, daidai yake da girmama shi kamar lokacin da yake da rai, babu banbanci. Kamar yadda ka san idan ka je gabansa yana raye za ka yi ladabi, haka ma yanzu idan ka je kabarinsa.

Yana daga girmama Manzon Allah (SAW) idan za ka ambaci sunansa, kar ka yi kamar na sauran mutane, ka sanya ladabi da natsuwa. Shi ya sa galibi masoyansa suka fi kiran mutanen da aka sanya musu sunansa (SAW) da lakabi. Maimakon Muhammadu, sai a rika fadar lakabin Nura, Hadi, Amin, Kamal, Nazir, Kamil da sauran su. Sannan da an ambaci sunan ka yi ma sa salati.

Haka nan yana daga girmama shi (SAW), idan mutum zai karanta Hadisinsa, ya yi shiga mai kyau tare da natsuwa da kankantar da kai. Haka nan ya girmama Sunnarsa.
Ma’anar Sunnah ita ce abin da Annabi (SAW) ya yi ko ya umurci a yi ko kuma aka yi a gabansa bai hana ba.
Amma ba kamar yadda wasu ke dauka ba musamman a kwanan nan, raina Allah da Manzonsa da wulakanta darajojin iyalan gidan Annabi (SAW) da sahabbansa a matsayin Sunnah.

Yana daga girmama Manzon Allah (SAW) da son sa, mutum ya rika shaukin jin tarihinsa da girmama iyalan gidansa da sahabbansa da malaman Musulunci magada Annabawa da duk wani abu da ya rataya da shi (SAW). Tun daga kan garin da ya zauna a ciki, da gidansa, da kayan da ya yi amfani da su har ma da ire-iren abincin da ya fi so da suturar sawa, duk a so su, a ga girmansu, ballantana kuma kabarinsa
Ya zo cikin Hadisi madaukaki cewa &kuot;Mumini ana binne shi ne a kasar da aka gina shi da ita.&kuot; Ma’ana duk inda aka binne mutum, da kasar wurin ne aka kwaba aka yi halittarsa da ita.
Kenan kasar Madina tana da matukar girma, don da ita ce aka gina Manzon Allah (SAW) da ita. Koda yake za a iya cewa ta yaya aka haife shi a Makka ba a Madina ba? To Abdullahi bin Abbas (RA) ya ruwaito Hadisin da cewa &kuot;lokacin da aka yi ruwan dufana ne Allah ya tafiyar da kasar halittarsa (SAW) zuwa Makka.&kuot;
Saboda haka kamar yadda Annabi (SAW) ya kasance mafificin Dan Adam, to kasar da aka yi halittarsa da ita ita ce mafificiyar kasa. Kuma shi ya sa Manzon Allah (SAW) ya ce &kuot;Ba domin yin Hijira – don Zatin Allah – ba (daga Makka zuwa Madina) da a Madina ma aka haife ni&kuot;. Tirmizi ya ruwaito Hadisin.
Domin fitar da abin a fili ma, Kakar-Kakar Manzon Allah (SAW) Salma’a wadda ta auri Hashimu ‘yar Madina ce daga kabilar Banin Najjar. Haka nan don Allah ya nuna wa mutane lamarin, sai Mahaifinsa Sayyidina Abdullahi (RA) ya zo ya rasu a Madina a lokacin da ya ziyarci dangin Kakarsa Salma’a. A da akwai gidan da ake zuwa ana ziyarar kabarin Kafin Ahlu Sa’ud su kama Madina su rufe wurin.
Ita ma Mahaifiyarsa Sayyida Amina (RA) ta ziyarci mijinta, Baban Annabi (SAW) tare da shi, da Ummu Aimana, a kan hanyarta ta komawa daga Madina ta rasu a Ab’wa. Daga Madina zuwa Ab’wa kilomita 150 ne. Amma tsakanin wurin da Makka kilomita 250.
Ibn Baddalu ya ce &kuot;Kamshin Madina ya ninka na ko ina&kuot;. Imamu Malik (RA) ya yi fatawa a yi wa wani mutum da ya ce kasar Madina lalatacciya ce bulala 30 kuma a kulle shi a kurkuku. Sai aka ce ma sa wannan mutumin babba ne fa? Sai ya ce &kuot;Ai ba bulala ya dace a yi ma sa ba, a daki wuyarsa kawai.&kuot; Ma’ana a kashe shi.
Akwai sabani a kan wadda ta fi daraja tsakanin Makka da aka haife shi (SAW) da Madina wadda ya yi Hijira kuma ya rasu a can. Ko wacce akwai Sahabbai da Malamai da suka goyi bayan fifikonta. Amma a wurin mu Malikawa, Madina ta fi daraja.
Sannan da Malikawan da sauran malaman Maz’habobin duk sun yi ittifakin cewa nan Shabbakin Manzon Allah (SAW) da ke kunshe da jikinsa ya fi ko wane wuri a kan kasa. An ciro wannan ne daga Tajuddinis subki. Shi kuma ya sake cirowa daga Ibn Akilul Hambali cewa &kuot;Wurin da aka binne Manzon Allah (SAW) ya fi har Al’arshi&kuot;.
Za mu dakata a nan sai Allah ya kai mu mako mai zuwa insha Allahu. Wa sallallahu alal fatihil khatimil hadiy wa ala alihi hakka kadirihi wa mikdarihil aziym.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yunwa Ba Dimokuradiya Ba Ce

Next Post

Kananan Sana’oi Da Ci Gaban Kasa

Related

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)
Dausayin Musulunci

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

1 day ago
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci
Dausayin Musulunci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

1 week ago
Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa
Dausayin Musulunci

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

3 weeks ago
Ramadan
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

4 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni

1 month ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci

1 month ago
Next Post
Kananan Sana’oi Da Ci Gaban Kasa

Kananan Sana’oi Da Ci Gaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

May 24, 2025
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

May 24, 2025
Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu

Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu

May 24, 2025
Mohamed Salah Ya Zama Gwarzon ÆŠan Wasan Firimiyar Ingila Na Bana

Mohamed Salah Ya Zama Gwarzon ÆŠan Wasan Firimiyar Ingila Na Bana

May 24, 2025
Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Yadda Za Ki Hada Garin Sakwara

Yadda Za Ki Hada Garin Sakwara

May 24, 2025
Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

May 24, 2025
NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

May 24, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata

May 24, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.