Gwamnan Jihar Borno Babagana Zulum,ya bada sanarwar bada tallafin karatu ga mata ‘yan asalin Jihar wadanda suka samu maki 2025, a jarabawar shiiga manyan makarantu wadda hukumar JAMB Ta shirya .
Zulum ya bayyana haka ne ranar Asabar ta maon daya gabata ;lokacin da aka yi bikin kaddamar da sababbin Shugabannin kungiyar kwararrun injiniyoyin mata ta Njeriya reshen Jihar Borno dake Babban Birnin Jihar Maiduguri,a gidan gwamnati na Jihar, da kuma tallafin karatu ga dalibai mata 12 wanda matar gwamnan ta yi.
- Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu
- Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar
APWEN wata kafa ce da take bda dama domin jajircewa wajen a tabbatar ana luara ba bada hakkin wasu,musamman ma lamarin daya shafi a mata cikin lamarin day shafi aikin Injiniya domin su bunksa da kuma jawo hankalin ‘yan mata su yi kokarin maida hankali wajen nazarin harkar kimiyya da fasahai.
Gwamnan ya bada tabbacin gwamnatinsa zata ci gaba da taimakawa ilimin ‘ya’ya mata, da kuma kara daukar nauyin mata da yawa su karanta bangaren da ya shafi kiwon lafiya,da kuma ilimin fasaha.
Ya ci gaba da jaddada“Cewa a wani kokari na bada kwarin gwiwa ga ilimin ‘ya’ya mata a Jihar,Ina son in bada sanarwar mata ‘yan salin Jihar wadanda suka samu 250 ko abinda yafi haka a jarabawar JAMB, gwamnatin Jihar Borno zata basu tallafi na su j e su yi nazarin daya shafi Fasaha/da ilimin koyar da sana’oi ko kimiyya, Fasaha,Injiniyarin da kuma Lissafi (STEM) kamar yadda Zulum ya bayyana,”.
Gwaman ya umarci mai rikon mukamin Shugaban ma’aikata, Hukumar bada tallafin karatu ta Jihar, ma’aikatar ilimi,da kuma kungiyar APWEN reshen Maiduguri cewar wadanda suka cika sharuddan da ake bukata ya dace a basu tallafin na karatu.
Lokacin taron ya taya Shugabnnin kungiyar amsu barin gado da kuma wadanda za su gaje su kan jajircewar da suka nuna wajen daukakalamarin da ya shafi kwararru ta bangaren Injiniya.
Da take gabatar da kasida mai taken, “Muhimmancin daukar nauyin da jawo hankalin’ ya’ya mata su yi karatun Injiniya da daukar abin a matsayin aiki a Nijeriya, ”Uwargidan gwamnan Borno,Dakta Habiba Babagana Zulum, ta lura da cewar daukar nauti wani lamari ne na yadda ake bunkasa ci gaban kwararru,inda ta yi nunu da cewa mata a Nijeriya sun samar da kashi 14 ne cikin 100 na ma’aikatan da suke da alaka da STEM, tace barin fiye da kashi 50 na yawan mutanen da basu da alaka da STEM wajen gina kasa wani abinda bai dace bane.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp