• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

by Abubakar Sulaiman
2 days ago
in Tsaro
0
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 60 A Borno

Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari kan wani wurin haƙar ma’adanai da ke Oreke-Oke Igbo a jihar Kwara a ranar Laraba, inda suka kashe ‘yansanda biyu tare da yin garkuwa da ma’aikata biyu, ciki har da wani ɗan ƙasar China. Waɗanda aka kashe su ne ASP Haruna Watsai da Inspector Tukur Ogah, waɗanda ke aiki a rundunar 45 PMF da ke Abuja kuma aka tura su wurin don samar da tsaro.

Kamar yadda Jami’ar hulɗa da Jama’a ta rundunar ‘Yansanda ta Jihar Kwara, Toun Ejire-Adeyemi ta bayyana, maharan sun kai harin ne da misalin ƙarfe 6:30 na yamma, inda suka bindige jami’an tsaron a kusa kuma suka tafi da bindigoginsu. Waɗanda aka sace su ne Mista Sam Xie Wie, wani ɗan ƙasar China, da Mista David Adenaiye, ɗan Nijeriya daga jihar Kogi. Dukansu suna aiki a wurin haƙar ma’adanan lokacin harin.

  • Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
  • Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Kwamishinan ‘Yansanda na Jihar Kwara, CP Adekimi Ojo, ya bayyana harin a matsayin mummunan abu, inda ya sha alwashin amfani da dukkan dabarun tsaro da bayanan sirri domin ceto waɗanda aka sace da kuma cafke waɗanda suka aikata laifin. Rundunar ta ce ana ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin tsaro da shugabannin al’umma don ƙarfafa tsaro da hana faruwar irin wannan hari a nan gaba.

An buƙaci mazauna yankin da su zauna lafiya kuma su kasance masu lura, yayin da ‘yansanda ke riƙon jama’a da su ba da sahihan bayanai da za su taimaka wajen ceton waɗanda aka sace da kuma gudanar da bincike. Rundunar ta kuma jaddada ƙudurinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin jihar Kwara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BindigaKwara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Next Post

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Related

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 60 A Borno

1 week ago
Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice
Tsaro

Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

1 week ago
Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci
Tsaro

Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci

1 week ago
Mummunan Hatsarin Mota Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 19 A Kogi
Tsaro

Mummunan Hatsarin Mota Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 19 A Kogi

2 weeks ago
Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2
Tsaro

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2

2 weeks ago
Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram 16 A Borno Bayan Sun Kawo Hari Barikinsu
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram 16 A Borno Bayan Sun Kawo Hari Barikinsu

2 weeks ago
Next Post
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta'adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Bindiga

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.