• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

by Abubakar Sulaiman
6 days ago
in Labarai
0
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Kaduna ta cafke mutane shida da ake zargi da aikata garkuwa da mutane, tare da ƙwato makamai daga hannunsu. An samu nasarar ne sakamakon atisayen haɗin gwuiwa da ‘yansanda suka gudanar a sassan jihohin Kaduna da Zamfara.

  • Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja
  • Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

Kakakin Rundunar ‘Yansanda ta Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa cewa lamarin ya samo asali ne daga wani rahoton gaggawa da wani mazaunin Ungwar Ninzom a Jagindi Tasha, ƙaramar hukumar Jama’a ya bayar ranar 22 ga Fabrairu, 2025, inda ya sanar da sace ɗansa, Hussaini Ibrahim, da wasu ‘yan bindiga suka yi.

Bayan samun rahoton, jami’an Ƴansanda daga sashin Kafanchan suka bazama don farautar masu garkuwa da mutanen. Koda yake an ce masu laifin sun tsere a farko, an ceto Hussaini daga dajin da ke kusa da yankin bayan kwana biyu, duk da cewa yana da raunin harbin bindiga a ƙafa. An ba shi kulawa a asibiti sannan aka mayar da shi ga iyalansa.

Bincike ya kai ga kama mutane huɗu: Umar Yusuf Jabiri (30), da Buhari Muhammad wanda aka fi sani da “General” (31), da Ahmadu Nasiru (51), da Zakari Saleh (50) — dukkansu mazauna Jagindi Tasha da Gidan Waya. Jami’an tsaro sun ƙwato bindiga AK-47 guda ɗaya da kuma wasu bindigogi uku ƙirar gida daga hannunsu.

A wani ci gaba kuma, bisa sahihan bayanan leƙen asiri, rundunar sashin yaƙi da garkuwa da mutane ƙarƙashin jagorancin CSP Sani Zuntu, ta gano wani kaya mai ɗauke da bindiga ƙirar AK-47 da aka ɓoye cikin buhu daga Jos, Jihar Filato zuwa Gusau, Jihar Zamfara.

Labarai Masu Nasaba

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

Hakan ya haifar da cafke Abdulmumin Sani da Naziru Musa a Gusau, inda ake zargin sun je karɓar bindigar. Rundunar ta ce za a gurfanar da su kotu bayan kammala bincike. Kwamishinan Ƴansanda na jihar, CP Rabiu Muhammad, ya yaba da ƙwazon jami’an da suka gudanar da waɗannan atisayen tare da tabbatar wa da jama’a cewa rundunar ba za ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen kawar da ‘yan ta’adda daga jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

Next Post

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Related

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye
Manyan Labarai

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

30 minutes ago
Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa
Labarai

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

1 hour ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

12 hours ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

13 hours ago
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
Labarai

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

18 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 01-07-2025

20 hours ago
Next Post
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

LABARAI MASU NASABA

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

August 2, 2025
Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

August 2, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.