• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɓaraka:, Ƴan Adawa, Shugabannin APC Na Shirya Kafa Sabuwar Tafiya — Lukman

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
in Siyasa
0
Ɓaraka:, Ƴan Adawa, Shugabannin APC Na Shirya Kafa Sabuwar Tafiya — Lukman
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC na Yankin Arewa-Maso-Yamma, Salihu Lukman, ya bayyana cewa jam’iyyun adawa da wasu shugabannin APC sun fara tattaunawa kan samar da sabuwar tafiyar siyasa kafin zaɓen 2027.

Lukman ya ce yawancin ‘yan siyasa na Nijeriya ba su yarda da tsari mai na gasar ko gogayya ba, suna fifita biyan buƙatun kansu wajen neman mulki ta hanyar danniya da maguɗi.

  • Nan Ba Da Jimawa Ba Za Mu Fara Zawarcin Kwankwaso – PDP
  • PDP Ta Nemi Tinubu Ya Binciki N25trn Da Ake Zargin Shugabannin APC Sun Sace

A cikin sakonsa na sabuwar shekara, ya jaddada cewa shugabanni na gari ya kamata su ba wa gasar siyasa dama don tabbatar da sahihancin shugabanci a kowane mataki.

Ya kuma kira ‘yan Nijeriya su tashi tsaye don ganin an kawar da APC a 2027 tare da samar da shugabanni masu son ci gaban ƙasa. Lukman ya ce dole ne a samar da jam’iyya mai mutunta dokokinta, wadda za ta bambanta da APC, PDP, LP, NNPP da sauran jam’iyyun da ake da su.

“Samar da irin wannan jam’iyya na da wahala, amma zaɓinmu shi ne mu koma kan hanya ta siyasa da ake gogayya domin samun shugabanni na gari, tare da daina dogaro da ‘yan siyasar da suka jefa ƙasar cikin wannan hali,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum

Lukman ya ce akwai yiwuwar Nijeriya ta gyara tsarin siyasa, ta hanyar samar da shugabanni da za su yi wa al’umma hidima, tare da mayar da ƙasar cikin jerin ƙasashe masu cigaba. Ya yi kira da a fara tunanin sabon tsarin siyasa mai ƙarfin haɗin kai da ƙwazo, domin sake fasalin Nijeriya kafin 2027.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Siyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Jawabin Shugaba Xi Ya Fayyace Manyan Nasarorin Da Sin Ta Samu A 2024

Next Post

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Da Uwargidansa Sun Aike Da Katin Murnar Shiga Sabuwar Shekara Ga Wakilan Malamai Da Dalibai A Amurka

Related

‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna
Labarai

‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

5 hours ago
Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum
Labarai

Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum

1 day ago
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC
Manyan Labarai

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

2 days ago
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde
Labarai

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

3 days ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

6 days ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

1 week ago
Next Post
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Da Uwargidansa Sun Aike Da Katin Murnar Shiga Sabuwar Shekara Ga Wakilan Malamai Da Dalibai A Amurka

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Da Uwargidansa Sun Aike Da Katin Murnar Shiga Sabuwar Shekara Ga Wakilan Malamai Da Dalibai A Amurka

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

July 19, 2025
Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

July 19, 2025
Mutuwar Malamin Jami’a A Otel: Jami’ar Kogi Za Ta Gudanar Da Bincike

Mutuwar Malamin Jami’a A Otel: Jami’ar Kogi Za Ta Gudanar Da Bincike

July 19, 2025
Dalilin Ciwon Baya Yayin Goyon Ciki Da Hanyar Magance Shi

Dalilin Ciwon Baya Yayin Goyon Ciki Da Hanyar Magance Shi

July 19, 2025
UTME

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

July 19, 2025
Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

July 19, 2025
‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

July 19, 2025
Abinci

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

July 19, 2025
sallah

Yadda Hauhawar Farashin Kayan Abinci Ya Ragu A Nijeriya

July 19, 2025
Shettima

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

July 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.