KASUWANCI
Bankin Masana’antu Ya Shawarci Matasa A Kan Rungumar Kirkire-Kirkire

Bankin Masana’antu BOI ya shawarci matasan kasar nan su samar da kirkire-kirkire son bayar da tasu gudunmawar wajen ciyar da kasar nan gaba. Jami’in reshen bankin na Osogbo Dakota Emmanuel Ojoowuro he ya bayar da shawarar a hirarsa da manema labarai a taron wayar da kai ya shiryawa masu matsakaitan sana’oi dake jihar Osun. Ya shawarci matsan su zurfafa yin tunani akan yadda zasu taimaki Kansu da kuma alumna, musamman son magance kalubaken sake a alkaryar su. Ojoowuro ya ce, akwai bukatar matasan su rungumi fannin kirkire-kirkire son bayar da tasu gudunmawar ga alkaryar su. Ya yi nuni da cewar, akwai matakai hudu da ya kamata su fara , da suka hadada, alfanu, yin kirkirar da kuma tunanin abinda zasu kirkira. Ya ce, bankin yana bayar da France ga matasa kuma baida wani wahakar samu. Ya ce, muna mayar da hanakali ga matasa domin a yanzu me Duke tasowa. Ya ce, an kuma samar masu da tsare-tsare yadda zasu iya samun dance a cikin sauki kuma duk wanda take son yin wani kirkire-kirkire zai iya zuwa bankin. Shima a nasa jawabin, Manajan Tuntuba na kamfanin Romis Mista Babatunde Bello, wanda kamfanin masu ya shirya taron ya ce, ta hanyar wannan taron mahalarta taron za’a basu shawarwari son inganta kasuwancin su. Ya ce, abinda muke yi shine, tallafawa masu matsakaitan sana’oi dake kasar nan akan yadda zasu infanta kasuwandin su. A karshe ya ce, a baya mun taimakawa mutane da dama da kuma taimaka masu wajen samun rance data bankin masana’antu kuma bazamu gajiya akan yin hakan ba.”
-
HANTSI1 day ago
Atiku Barazanar APC
-
RAHOTANNI1 day ago
Ba Mu Da Masaniyar Cafke Wani Da Sakamakon Zabe Na Bogi A Abia, Cewar ‘Yan Sanda
-
MANYAN LABARAI2 days ago
Dage Zabe: Ka Da Mu Karaya Akwai Fata –Saraki Ga Al’ummar Nijeriya
-
KASASHEN WAJE13 hours ago
Mayakan Boko Haram 187 Sun Ajje Makamai A Kamaru
-
BUDADDIYAR WASIKA1 day ago
Baba Buhari, Mu Na Murna Da Tazarce
-
LABARAI2 days ago
Dage Zabe: Ba Karamin Mamaki Abun Ya Bani Ba –Atiku
-
LABARAI11 hours ago
Wani Kusa A APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Bauchi
-
MANYAN LABARAI1 day ago
Ko A Dage Zabe Ko Kada A Dage Sai Mun Kayar Da Buhari, In Ji Kera