ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Atiku da Gwamnan Bauchi Sun Sasanta Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

by Sadiq
3 years ago
Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, da gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, sun sasanta rikicin da ke tsakaninsu, tare da kudurin yin aiki tare domin samun nasarar zabe a babban zaben badi. 

A baya LEADERSHIP ta rawaito cewa Gwamna Mohammed, ya ce ba zai yi kasa a gwiwa ba wajen ficewa daga kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar PDP na shugaban kasa idan har dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ya gaza fitowa fili ya karyata wadanda ke yi masa aiki tare da bayyana goyon bayansa na sake tsayawa takara a karo na biyu a Jihar Bauchi.

  • 2023: Gwamnan Akwa Ibom Ya Karyata Ajiye Mukaminsa Na Shugaban Yakin Zaben Atiku Da Okowa
  • Yin Amfani Da Yanar Gizo Wajen Raya Duniya

Mohammed, wanda shi ne mataimakin shugaban jam’iyyar a Arewa, ya bayyana haka a wata wasika mai shafi takwas da ya aike wa shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Sanata Dr. Iyiocha Ayu.

ADVERTISEMENT

Ayu da wasu jiga-jigan jam’iyyar sun yi gaggawar kai wa gwamnan Jihar Bauchi ziyara a kwanakin baya.

Duk da cewa taron a sirri aka yi, shugabannin jam’iyyar sun yi watsi da duk wani ra’ayi na sabon rikici a tsakaninsu.

LABARAI MASU NASABA

Cikin Sauƙi Na Yanke Shawarar Komawa APC – Gwamna Fubara

Ba Zan Taɓa Komawa Jam’iyyar APC Ba — Abaribe

A ci gaba da taron na Bauchi Atiku ya kuma yi wata ganawa da Gwamna Mohammed da wasu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a Abuja a daren ranar Talata.

Da yake bayyana sakamakon taron Abuja da aka yi a safiyar ranar Laraba ta shafinsa na Facebook da aka tabbatar, Atiku ya rubuta cewa: “A daren jiya na karbi bakuncin wasu daga cikin jiga-jigan jam’iyyarmu ta PDP a Abuja, mun tattauna halin da jam’iyyarmu da al’ummar kasar nan ke ciki, kuma muka sake komawa kan lamarin don aikin kishin kasa don murmurewa da dawo da Nijeriya don dawo kasa turbar daidai. – AA.”

Idan dai ba a manta ba PDP ta yi ta fafatawa da kungiyar gwamnoni biyar (PDP G5) wato gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Ezenwo Wike da takwarorinsa na Abia, Oyo, Enugu da Jihar Benue, Okezie Ikpeazu, Seyi Makinde, Ifeanyi Ugwuanyi. da Samuel Ortom.

A baya-bayan nan dai sun kara zafafa adawa da yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Siyasa

Cikin Sauƙi Na Yanke Shawarar Komawa APC – Gwamna Fubara

December 18, 2025
Ba Zan Taɓa Komawa Jam’iyyar APC Ba — Abaribe
Siyasa

Ba Zan Taɓa Komawa Jam’iyyar APC Ba — Abaribe

December 16, 2025
El-Rufai Ya Ƙaryata Rahoton Goyon Bayan Yanki Ko Wani Mutum A Zaɓen 2027
Siyasa

El-Rufai Ya Ƙaryata Rahoton Goyon Bayan Yanki Ko Wani Mutum A Zaɓen 2027

December 15, 2025
Next Post
Dan Wasan Senegal Mane Ba Zai Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ba Saboda Rauni 

Dan Wasan Senegal Mane Ba Zai Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ba Saboda Rauni 

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.