ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Daga Karshe Dai Tawagar Su Dogara Sun Mara Wa Atiku Baya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
2023

Kungiyar jagororin kiristoci da musulmai ‘yan siyasa da suka fito daga jihohin arewa 19 da babban birnin tarayya Abuja sun ayyana goyon bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023 da ke tafe, Alhaji Atiku Abubakar a matsayin dan takarar da suka cimma matsayar mara wa baya.

Kungiyar wacce ta misalta goyon bayan tikitin takarar Atiku/Okowa a matsayin zabin da ya dace ga dukkanin masu neman adalci ga kowani bangare a kasar nan.

  • Dogara, Babachir Sun Gana Da Shugabannin Kiristoci Don Daukar Matsaya Kan Zaben 2023
  • Rayuwata Na Cikin Hatsari, Ana Kokarin Kashe Ni – Yakubu Dogara

Wannan matsayar na kunshe ne ta cikin wata sanarwar bayan taro da kungiyar jagororin suka yi a Abuja a ranar Juma’a dauke da sanya hannun tsohon shugaban marasa rinjaye na majalisar wakilai Hon. Mohammed Umara Kumalia da Barista Nunge Mele, (SAN) tare da raba kwafinta ga ‘yan jarida a Bauchi.

ADVERTISEMENT

Idan za ku iya tunawa dai, gungun kiristocin wadanda suke karkashin tawagar su tsohon Kakakin majalisar tarayya, Yakubu Dogara wadanda suka kasance mambobin jam’iyyar APC ne a baya, sun yi ta gwagwarmayar yaki da tikitin Musulmi da Musulmi wanda suka sha alwashin ba za su mara wa dan takarar jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu baya ba.

Sanarwar kungiyar ya nemi dukkanin al’ummar Nijeriya da su mara wa PDP baya domin bai wa kowani bangare dama a cikin mulki a maimakon nuna wariya ga kiristoci ta hanyar yin tikiri musulmai biyu da APC ta yi.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

Sun yi tilawar cewa, kungiyar jagororin kiristoci da musulmai a arewa ta kafa wani kwamiti a ranar 8 ga watan Oktoba domin ya yi nazarin dan takarar da ya dace a mara wa baya cikin manyan ‘yan takarar shugaban kasa a zaben 2023 da ke tafe.

Kungiyar ta ce, a bisa nazarinta da bincikenta, tikitin takarar Atiku Abubakar na PDP ne kawai ya fi zama a’ala ga dukkanin al’ummar Nijeriya, kuma shine wanda ya fi dacewa a duk cikin manyan ‘yan takarar shugaban kasa guda hudu da suke nema a halin yanzu.

Daga bisani kungiyar sun sha alwashin cewa za su kasa su tsare har sai sun tabbatar APC ba ta samu nasara a zaben 2023 ba, domin a cewarsu an kitsa rashin adalci ga al’ummar kiristoci a yadda aka fitar da tsarin tikitin jam’iyyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Next Post
Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.