• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ko INEC Za Ta Iya Gudanar Da Sahihin Zabe?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2023: Ko INEC Za Ta Iya Gudanar Da Sahihin Zabe?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata ne, shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Mammod Yakubu ya yi alkawarin cewa duk da kalubalen da hukumarsa kefuskanta, za ta gudanar da sahihin zabe mai cike da adalci a 2023.

Ya ce, ‘kuri’un ‘yan Nijeriya ne kadai zai tabbatar da wanda ya lashe zabe a 2023, wannan shi ne kokarinmu ga kasar nan,” in ji Farfesa Yakubu.

  • Shekara 62 Da Samun ‘Yancin Kai: Na Damu Da Halin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki – Buhari
  • Darajar Vinicius Junior Ta Sake daukaka

Ko kalamun Farfesa Yakubu zai iya shugabantar INEC wajen gudanar da sahihin zabe a 2023, musamman ma zaben shugaban kasa?.

Dukkan zaben shugaban kasa a Nijeriya yana da matukar muhimmanci da kuma rudani. Ko shakka babu samun cikakken zaman lafiya da hadin kai a Nijeriya ya ta’allaka ne da sakamakon zaben shugaban kasa a 2023.

Gaskiyar lamari shi ne, mutanen Nijeriya suna bukatar fita daga kangin mummunan shugabanci da suka samu kansu a ciki.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

A baya, matasa suna nuna halin-ko-in-kula a kan harkokin zabe, amma a wannan lokaci matsa ne suka fi yawa wajen amsar katin zabe a rajistar INEC na zaben 2023.

A yanzu haka matasan Nijeriya sun farka daga dogon baccin da suke yi wajen shiga a dama da su kan harkokin zabe, inda suka sha alkawashin tsunduma a al’amuran zaben shugaban kasa a 2023.

Lallai shigan matasa cikin harkokin zabe gadan-gadan zai samar da sabon sauyi a cikin siyasar Nijeriya.

Saboda haka, hukumar INEC ba ta da wani zabi illa ta yi kokarin gudanar da sahihin zaben shugaban kasa a watan Fabrairun 2023. Dole INEC ta tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya ne suka zabi shugaban kasa da hannunsu.

Dokar zabe ta 2022 ta tanadi cewa dole a yi amfani da na’ura wajen bayyana sakamakon. Ko shakka babu amfani da na’ura wajen bayyana sakamakon zabe zai rage magudin zabe.

Wannan ta sa dole INEC ta sake kokari wajen kara ma’aikata da sauran kayayyakin zabe na zamani saboda a samu abin da ake bukata.

Masu sharhin harkokin siyasa dai suna ganin cewa hukumar zabe ba za ta iya gudanar da sahibhin zabe ba har sai ta samu jajirtaccen wakilai a jihohi.

Indan har hukumar zabe tana son gudanar da sahihin zabe, to dole ta samu jajirtattun kwamishinoni zabe a dukkanin jihohin Nijeriya.

Ayyukan kwamishinonin zabe sun hada da kula da dukkan ayyukan ma’aikata na wajin-gadi na INEC da samar da cikakken sahihin sakamakon zabe.

Tambaya a nan shi ne wadannan kwamishinonin zabe da INEC take da su a yanzu za su iya taimaka mata wajen gudanar da shihin zabe?

Tabbas INEC za ta iya gudanar da sahihin zabe idan ta samu wakilan da za su taimaka mata.

Ya kamata INEC ta yi kokarin tsaftace ma’aikatanta wajen samun nasarar gudanar da sahihin zabe a 2023.

Babu wata hukumar gwamnati da mutane suke da gwarin gwiwa kamar INEC, musamman ma idan aka samu sahihin zabe a 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECKuri'aSiyasaYakubuZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Atiku Ya Karyata Batun Zai Goyi Bayan Wike A Zaben 2027

Next Post

Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.