• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ko INEC Za Ta Iya Gudanar Da Sahihin Zabe?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2023: Ko INEC Za Ta Iya Gudanar Da Sahihin Zabe?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata ne, shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Mammod Yakubu ya yi alkawarin cewa duk da kalubalen da hukumarsa kefuskanta, za ta gudanar da sahihin zabe mai cike da adalci a 2023.

Ya ce, ‘kuri’un ‘yan Nijeriya ne kadai zai tabbatar da wanda ya lashe zabe a 2023, wannan shi ne kokarinmu ga kasar nan,” in ji Farfesa Yakubu.

  • Shekara 62 Da Samun ‘Yancin Kai: Na Damu Da Halin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki – Buhari
  • Darajar Vinicius Junior Ta Sake daukaka

Ko kalamun Farfesa Yakubu zai iya shugabantar INEC wajen gudanar da sahihin zabe a 2023, musamman ma zaben shugaban kasa?.

Dukkan zaben shugaban kasa a Nijeriya yana da matukar muhimmanci da kuma rudani. Ko shakka babu samun cikakken zaman lafiya da hadin kai a Nijeriya ya ta’allaka ne da sakamakon zaben shugaban kasa a 2023.

Gaskiyar lamari shi ne, mutanen Nijeriya suna bukatar fita daga kangin mummunan shugabanci da suka samu kansu a ciki.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

A baya, matasa suna nuna halin-ko-in-kula a kan harkokin zabe, amma a wannan lokaci matsa ne suka fi yawa wajen amsar katin zabe a rajistar INEC na zaben 2023.

A yanzu haka matasan Nijeriya sun farka daga dogon baccin da suke yi wajen shiga a dama da su kan harkokin zabe, inda suka sha alkawashin tsunduma a al’amuran zaben shugaban kasa a 2023.

Lallai shigan matasa cikin harkokin zabe gadan-gadan zai samar da sabon sauyi a cikin siyasar Nijeriya.

Saboda haka, hukumar INEC ba ta da wani zabi illa ta yi kokarin gudanar da sahihin zaben shugaban kasa a watan Fabrairun 2023. Dole INEC ta tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya ne suka zabi shugaban kasa da hannunsu.

Dokar zabe ta 2022 ta tanadi cewa dole a yi amfani da na’ura wajen bayyana sakamakon. Ko shakka babu amfani da na’ura wajen bayyana sakamakon zabe zai rage magudin zabe.

Wannan ta sa dole INEC ta sake kokari wajen kara ma’aikata da sauran kayayyakin zabe na zamani saboda a samu abin da ake bukata.

Masu sharhin harkokin siyasa dai suna ganin cewa hukumar zabe ba za ta iya gudanar da sahibhin zabe ba har sai ta samu jajirtaccen wakilai a jihohi.

Indan har hukumar zabe tana son gudanar da sahihin zabe, to dole ta samu jajirtattun kwamishinoni zabe a dukkanin jihohin Nijeriya.

Ayyukan kwamishinonin zabe sun hada da kula da dukkan ayyukan ma’aikata na wajin-gadi na INEC da samar da cikakken sahihin sakamakon zabe.

Tambaya a nan shi ne wadannan kwamishinonin zabe da INEC take da su a yanzu za su iya taimaka mata wajen gudanar da shihin zabe?

Tabbas INEC za ta iya gudanar da sahihin zabe idan ta samu wakilan da za su taimaka mata.

Ya kamata INEC ta yi kokarin tsaftace ma’aikatanta wajen samun nasarar gudanar da sahihin zabe a 2023.

Babu wata hukumar gwamnati da mutane suke da gwarin gwiwa kamar INEC, musamman ma idan aka samu sahihin zabe a 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECKuri'aSiyasaYakubuZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Atiku Ya Karyata Batun Zai Goyi Bayan Wike A Zaben 2027

Next Post

Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.