• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ko INEC Za Ta Iya Gudanar Da Sahihin Zabe?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2023: Ko INEC Za Ta Iya Gudanar Da Sahihin Zabe?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata ne, shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Mammod Yakubu ya yi alkawarin cewa duk da kalubalen da hukumarsa kefuskanta, za ta gudanar da sahihin zabe mai cike da adalci a 2023.

Ya ce, ‘kuri’un ‘yan Nijeriya ne kadai zai tabbatar da wanda ya lashe zabe a 2023, wannan shi ne kokarinmu ga kasar nan,” in ji Farfesa Yakubu.

  • Shekara 62 Da Samun ‘Yancin Kai: Na Damu Da Halin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki – Buhari
  • Darajar Vinicius Junior Ta Sake daukaka

Ko kalamun Farfesa Yakubu zai iya shugabantar INEC wajen gudanar da sahihin zabe a 2023, musamman ma zaben shugaban kasa?.

Dukkan zaben shugaban kasa a Nijeriya yana da matukar muhimmanci da kuma rudani. Ko shakka babu samun cikakken zaman lafiya da hadin kai a Nijeriya ya ta’allaka ne da sakamakon zaben shugaban kasa a 2023.

Gaskiyar lamari shi ne, mutanen Nijeriya suna bukatar fita daga kangin mummunan shugabanci da suka samu kansu a ciki.

Labarai Masu Nasaba

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

A baya, matasa suna nuna halin-ko-in-kula a kan harkokin zabe, amma a wannan lokaci matsa ne suka fi yawa wajen amsar katin zabe a rajistar INEC na zaben 2023.

A yanzu haka matasan Nijeriya sun farka daga dogon baccin da suke yi wajen shiga a dama da su kan harkokin zabe, inda suka sha alkawashin tsunduma a al’amuran zaben shugaban kasa a 2023.

Lallai shigan matasa cikin harkokin zabe gadan-gadan zai samar da sabon sauyi a cikin siyasar Nijeriya.

Saboda haka, hukumar INEC ba ta da wani zabi illa ta yi kokarin gudanar da sahihin zaben shugaban kasa a watan Fabrairun 2023. Dole INEC ta tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya ne suka zabi shugaban kasa da hannunsu.

Dokar zabe ta 2022 ta tanadi cewa dole a yi amfani da na’ura wajen bayyana sakamakon. Ko shakka babu amfani da na’ura wajen bayyana sakamakon zabe zai rage magudin zabe.

Wannan ta sa dole INEC ta sake kokari wajen kara ma’aikata da sauran kayayyakin zabe na zamani saboda a samu abin da ake bukata.

Masu sharhin harkokin siyasa dai suna ganin cewa hukumar zabe ba za ta iya gudanar da sahibhin zabe ba har sai ta samu jajirtaccen wakilai a jihohi.

Indan har hukumar zabe tana son gudanar da sahihin zabe, to dole ta samu jajirtattun kwamishinoni zabe a dukkanin jihohin Nijeriya.

Ayyukan kwamishinonin zabe sun hada da kula da dukkan ayyukan ma’aikata na wajin-gadi na INEC da samar da cikakken sahihin sakamakon zabe.

Tambaya a nan shi ne wadannan kwamishinonin zabe da INEC take da su a yanzu za su iya taimaka mata wajen gudanar da shihin zabe?

Tabbas INEC za ta iya gudanar da sahihin zabe idan ta samu wakilan da za su taimaka mata.

Ya kamata INEC ta yi kokarin tsaftace ma’aikatanta wajen samun nasarar gudanar da sahihin zabe a 2023.

Babu wata hukumar gwamnati da mutane suke da gwarin gwiwa kamar INEC, musamman ma idan aka samu sahihin zabe a 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECKuri'aSiyasaYakubuZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Atiku Ya Karyata Batun Zai Goyi Bayan Wike A Zaben 2027

Next Post

Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

3 hours ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

4 hours ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

5 days ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

7 days ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

1 week ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

1 week ago
Next Post
Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.