ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ko INEC Za Ta Iya Gudanar Da Sahihin Zabe?

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
INEC

A makon da ya gabata ne, shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Mammod Yakubu ya yi alkawarin cewa duk da kalubalen da hukumarsa kefuskanta, za ta gudanar da sahihin zabe mai cike da adalci a 2023.

Ya ce, ‘kuri’un ‘yan Nijeriya ne kadai zai tabbatar da wanda ya lashe zabe a 2023, wannan shi ne kokarinmu ga kasar nan,” in ji Farfesa Yakubu.

  • Shekara 62 Da Samun ‘Yancin Kai: Na Damu Da Halin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki – Buhari
  • Darajar Vinicius Junior Ta Sake daukaka

Ko kalamun Farfesa Yakubu zai iya shugabantar INEC wajen gudanar da sahihin zabe a 2023, musamman ma zaben shugaban kasa?.

ADVERTISEMENT

Dukkan zaben shugaban kasa a Nijeriya yana da matukar muhimmanci da kuma rudani. Ko shakka babu samun cikakken zaman lafiya da hadin kai a Nijeriya ya ta’allaka ne da sakamakon zaben shugaban kasa a 2023.

Gaskiyar lamari shi ne, mutanen Nijeriya suna bukatar fita daga kangin mummunan shugabanci da suka samu kansu a ciki.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

A baya, matasa suna nuna halin-ko-in-kula a kan harkokin zabe, amma a wannan lokaci matsa ne suka fi yawa wajen amsar katin zabe a rajistar INEC na zaben 2023.

A yanzu haka matasan Nijeriya sun farka daga dogon baccin da suke yi wajen shiga a dama da su kan harkokin zabe, inda suka sha alkawashin tsunduma a al’amuran zaben shugaban kasa a 2023.

Lallai shigan matasa cikin harkokin zabe gadan-gadan zai samar da sabon sauyi a cikin siyasar Nijeriya.

Saboda haka, hukumar INEC ba ta da wani zabi illa ta yi kokarin gudanar da sahihin zaben shugaban kasa a watan Fabrairun 2023. Dole INEC ta tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya ne suka zabi shugaban kasa da hannunsu.

Dokar zabe ta 2022 ta tanadi cewa dole a yi amfani da na’ura wajen bayyana sakamakon. Ko shakka babu amfani da na’ura wajen bayyana sakamakon zabe zai rage magudin zabe.

Wannan ta sa dole INEC ta sake kokari wajen kara ma’aikata da sauran kayayyakin zabe na zamani saboda a samu abin da ake bukata.

Masu sharhin harkokin siyasa dai suna ganin cewa hukumar zabe ba za ta iya gudanar da sahibhin zabe ba har sai ta samu jajirtaccen wakilai a jihohi.

Indan har hukumar zabe tana son gudanar da sahihin zabe, to dole ta samu jajirtattun kwamishinoni zabe a dukkanin jihohin Nijeriya.

Ayyukan kwamishinonin zabe sun hada da kula da dukkan ayyukan ma’aikata na wajin-gadi na INEC da samar da cikakken sahihin sakamakon zabe.

Tambaya a nan shi ne wadannan kwamishinonin zabe da INEC take da su a yanzu za su iya taimaka mata wajen gudanar da shihin zabe?

Tabbas INEC za ta iya gudanar da sahihin zabe idan ta samu wakilan da za su taimaka mata.

Ya kamata INEC ta yi kokarin tsaftace ma’aikatanta wajen samun nasarar gudanar da sahihin zabe a 2023.

Babu wata hukumar gwamnati da mutane suke da gwarin gwiwa kamar INEC, musamman ma idan aka samu sahihin zabe a 2023.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.