• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ko Yawan Masu Rajistar Zabe Zai Iya Tasiri Ga ‘Yan Takara?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2023: Ko Yawan Masu Rajistar Zabe Zai Iya Tasiri Ga ‘Yan Takara?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 31 ga watan Yuli ne, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana kammala rajistar mallakar katin zabe da ta bude a ranar 28 ga Yunin 2020, shekara biyu kenan da wata guda. 

Bayan kammala rajistar, hukumar ta ce ta yi sabbin rajista ga ‘yan Nijeriya miliyan 12, 298, 944. Kafin nan akwai masu rajista har mutum 84, 000, 484.

  • Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai
  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Wato a yanzu akwai wadanda suka mallaki katin zabe har miliyan 96, 299, 428 kenan.

A bayanan da hukumar INEC ta fitar har yanzu Kano da Legas ke da mafi yawan masu rajista.

Jihohi uku da ke kan gaba wajen yawan wadanda suka yi rajista kwanan nan, sun hada da Legas da ke da mutum 585,629.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Sai Kano mai 569, 103. Ta uku it ace Jihar Delta mai mutum 523, 517. Jihohi masu karancin wadanda suka yi rajista kwanan nan su ne: Ekiti da ke da mutum 124, 844.

Mai bi mata ita ce Jihar Yobe mai mutum 152, 414. Sai Babban Birnin Tarayya (FCT), Abuja mai mutum 211, 341.

A wannan kididdigan ya nuna cewa yankin Kudu sun fi yankin Arewa karin masu rajistar, alamu na kuma nuna cewa kowani bangare zai iya yin dan bangarensa ne a zaben 2023.

Amma dai ba a nan gizo ke sakar ba, daga bibiyar yawan masu rajistar zabe, za a fahimci ‘yan takarar jam’iyyar APC da PDP har yanzu su ne a sahun gaban wajen yiwuwar lashe zabe.

Amma fa karfin yunkurowar da Kwankwaso na NNPP da Obi na LP za su iya kawo wa nasarar Atiku cikas sosai.

Haka kuma za su iya hana Tinubu lashe zabe kaitsaye. Sakamakon zaben Ekiti da Osun na gwamna da kuma zabukan cike gurbi na jihohi da tarayya sun nuna APC da PDP dai ne manyan ‘yan takara.

Idan a bi ta barawo, to a bi ta ma bi sahu, kamar yadda masu iya magana suke cewa tun bayan kafuwar jam’iyyar NNPP mai kayan marmari na Kwankwas, gaba daya tasirin jam’iyyar PDP ya mutu a Kano.

Ita kanta jam’iyya mai mulki a Kano ta kasa tsayuwa da kafafuwanta don ta shiga rudani har wasu jiga-jiganta suka shiga NNPP irin su Malam Ibrahim Shekarau, Sanata kuma Tsohon Gwamna a jihar.

Kasancewar a duk arewacin Nijeriya, Jihar Kano ce aka fi samun yawan kuri’u, kenan akwai yiwuwar Kwankwaso zai iya yi wa duk wata jam’iyya illa a jihar.

Masu sharhi kan siyasa sun hasaso cewa duk dan takarar da bai samu nasara a jihohin Kano ko Legas ko Kaduna ba, ko shakka babu zai wahala ya iya samun nasara a zaben 2023 na shugaban kasa.

A Kaduna ma nan ana ganin Gwamna Nasir El-Rufai ya janyo wa jam’iyyar APC bakin jini. Sannan kuma dan Jihar Kaduna ne mataimakin takarar Peter Obi na jam’iyyarr LP; wato Yusuf Datti Baba-Ahmed, ko ba komai a jihar LP za ta iya jan wasu kaso na kuri’u da za a jefa.

Idan aka koma kudu maso kudu kuwa, sanin kowa ne jam’iyyar APC ba ta da wani tasiri a yankin. Mutanen yankin sun so a ce Gwamna Wike ne dan takarar PDP ba Atiku Abubakar ba.

Dalili kenan PDP ta kasa barci tana so sai ta lallashi Gwamna Nysome Wike daga fushin da ya yi. Dama kuma yankin na PDP ne tun filazal.

Haka kuma rashin bai wa dan kudu maso gabas takara da PDP ko APC suka yi, ya sa jihohin Igbo sun karkata ga dansu Peter Obi na jam’iyyar LP.

Idan kuwa aka koma ma’anar siyasa za a ga cewa, siyasa hanya ce da mutane ke bi wajen rayuwa a hade, ko a tare ko a kungiyance cikin manufa daya.

Siyasa na nufin hada yarjejeniya tsakanin mutane domin su zauna tare duk da mabam-bantan ra’ayoyi, kabilu da addinai, a birane da kasashe.

Bisa wannan ta’arifin na siyasa a yanayin da ake tafiya a Nijeriya, kowani bangare ko yanki nasu suke yi.

Kenan yankin kudu sun yunkuro a wannan karo ta la’akari da samun yawan masu rajistan katin zabe. Da can sun san yankin arewa ba yinsu suke yi ba.

Kuma a yanzu yankin arewa za a yi masu illa game da rarrabuwan ‘yan takara da aka samu a yankin. Ko ma dai mene ne, Hausawa na cewa ‘ba a san ma ci tuwo ba, sai miya ta kare’.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023Kuri'aMasu Kada Kuri'aShugabanniSiyasaTambarin DimokuradiyyaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Salman Rushdie: Wanda Ya Yi Batanci Ga Annabi Na Cikin Mawuyacin Hali Bayan Kai Masa Hari

Next Post

Martanin El-Rufa’i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

3 weeks ago
Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

3 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

3 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

4 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

4 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

4 weeks ago
Next Post
Martanin El-Rufa’i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba

Martanin El-Rufa'i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Majalisar Dokokin Nijeriya Sun Bukaci Karin Albashi

Yadda ‘Yan Majalisa Ke Cusa Ayyuka Marasa Amfani A Kasafin Kuɗi – Rahoto

May 22, 2025
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

May 22, 2025
‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

May 21, 2025
Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

May 21, 2025
Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

May 21, 2025
Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

May 21, 2025
Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

May 21, 2025
Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

May 21, 2025
Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

May 21, 2025
Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

May 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.