• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Lauyoyi Sun Murza Gashin Baki Kan Sauya Halattattun ‘Yan Takara Da Wasu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
Dalilinmu Na Karbar Sunan Ahmed Lawan Maimakon Na Machina – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Lauyoyi da Kungiyoyin Fararen Hula sun murza gashin baki a kan cewa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta yi watsi da duk wani dan takarar da bai shiga zaben fid da gwani ba da jam’iyyun siyasa suka tura mata sunayensu.

Gamayyar kungiyoyin fararen hula sun zargi jam’iyyun siyasa da tura wa INEC da sunayen wasu ‘yan takara wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba a matsayin ‘yan takararsu tare da cire sunayen ‘yan takarar da suka lashe zaben fitar da gwani.

Binciken LEADERSHIP ya gano cewa jam’iyyar APC ta tura wa INEC sunayen manyen ‘yan siyasa wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba a matsayin ‘yan takararsu.

Gamayyar kungiyoyin sun siffanta lamarin da rashin adalci tare da bayyana cewa dole jam’iyyun siyasan su fuskanci hukunci domin kuwa kotu ta shirya tsaf wajen yakar irin wannan gurbatacciyar dimokuradiyya.

Da yake zantawa da LEADERSHIP, shugaban gamayyar kungiyoyin fararen huda, Awwal Musa Rafsanjani ya bayyana cewa bai kamata a bar ‘yan siyasa suna yin abin da suka ga dama ba. Ya kara da cewa su ne manyan wadanda suka fi amfana da dimokuradiyya kuma ne suke lalata ta.

Labarai Masu Nasaba

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Ya ce, “Wannan wasu dabi’u ne da gurbatattun ‘yan siyasa ke yi kuma INEC tana kara musu kwarin gwiwa a wajen gudanar da zaben fid da gwani, saboda ta yaya wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba a ba su damar tsayawa takara a babban zabe.

“Ya kamata ‘yan Nijeriya su dauki darasi a kan irin wannan lamari da suka faru a baya. Idan har irin wannan lamari ya taba faruwa a baya kuma kotu ta rushe zaben wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba, lalle kotu tana nan za ta zantar da hukunci a kan wannan mummunan dabi’a.

“Mutanen da suke gudanar da irin wannan lamari suna amfani ne da matsayinsu kuma ya kamata INEC ta yi watsi da irin wannan lamari.

“’Yan takara sun gudanar da zaben fid da gwani kuma har jami’an INEC sun halarci wurin tare da saka ido da amincewa da sunayen wadanda suka samu nasara, sannan bai kamata a sauya sunayen wadanda suka shiga zaben fid da gwani ba da wasu ‘yan takara daban ba,”

Su ma kungiyar lauyoyi sun bayyana cewa lamarin Ahmad Lawan da Godswill Akpabio, a bayana yake na saba wa dokar zabe.

Manyan lauyoyin Nijeriya sun mayar da martani kan sauya sunayen wadanda suka lashe zaben fid da gwani, inda suka suffanta lamarin da take hakkin dokar zabe.

Babban lauya mai suna Kayode Enitan (SAN) ya bayyana cewa INEC ba za ta taba amincewa da sunayen ‘yan takarar da ba su shiga zaben fid da gwani ba, domin ya saba wa sashi na 31 da 33 na dokar zabe.

Ya ce, “Akwai hanyoyin sauya ‘yan takarar da suka lashe zaben fid da gwani kamar yadda sashi na 31 da 33 na dokar zabe ta tanada, ana iya sauya sunayen ne kadai idan dan takara ya mutu.

“Idan dan takarar da ya lashe zaben fid da gwani ya mutu, to dole ne jam’iyya ta sake gudanar da zaben fid da gwani.

“Amma haka kawai, INEC ba ta da hukumin sauya sunayen ‘yan takarar da suka lashe zaben fid da gwani, sai dai dan takara ya janye ko kuma ya mutu.”
Shi ma babban lauya mai suna Matthew Buka (SAN) ya bayyana cewa doka a bayyana take, domin doka ta tanadar da cewa babu wanda zai tsaya takarar babban zabe har sai ya lashe zaben fid da gwani a karkashin jam’iyyun siyasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Malamai Sun Yaba Wa Sarkin Sha’iran Kano Kan Yi Wa Ma’aiki Wakoki 2,000

Next Post

Ci Gaba Abu Ne Na Zahiri A Tarihin Sin

Related

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩
Manyan Labarai

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

11 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

11 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

12 hours ago
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma
Manyan Labarai

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

13 hours ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

15 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

17 hours ago
Next Post
Ci Gaba Abu Ne Na Zahiri A Tarihin Sin

Ci Gaba Abu Ne Na Zahiri A Tarihin Sin

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.