• English
  • Business News
Sunday, June 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Lauyoyi Sun Murza Gashin Baki Kan Sauya Halattattun ‘Yan Takara Da Wasu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
Dalilinmu Na Karbar Sunan Ahmed Lawan Maimakon Na Machina – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Lauyoyi da Kungiyoyin Fararen Hula sun murza gashin baki a kan cewa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta yi watsi da duk wani dan takarar da bai shiga zaben fid da gwani ba da jam’iyyun siyasa suka tura mata sunayensu.

Gamayyar kungiyoyin fararen hula sun zargi jam’iyyun siyasa da tura wa INEC da sunayen wasu ‘yan takara wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba a matsayin ‘yan takararsu tare da cire sunayen ‘yan takarar da suka lashe zaben fitar da gwani.

Binciken LEADERSHIP ya gano cewa jam’iyyar APC ta tura wa INEC sunayen manyen ‘yan siyasa wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba a matsayin ‘yan takararsu.

Gamayyar kungiyoyin sun siffanta lamarin da rashin adalci tare da bayyana cewa dole jam’iyyun siyasan su fuskanci hukunci domin kuwa kotu ta shirya tsaf wajen yakar irin wannan gurbatacciyar dimokuradiyya.

Da yake zantawa da LEADERSHIP, shugaban gamayyar kungiyoyin fararen huda, Awwal Musa Rafsanjani ya bayyana cewa bai kamata a bar ‘yan siyasa suna yin abin da suka ga dama ba. Ya kara da cewa su ne manyan wadanda suka fi amfana da dimokuradiyya kuma ne suke lalata ta.

Labarai Masu Nasaba

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

Ya ce, “Wannan wasu dabi’u ne da gurbatattun ‘yan siyasa ke yi kuma INEC tana kara musu kwarin gwiwa a wajen gudanar da zaben fid da gwani, saboda ta yaya wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba a ba su damar tsayawa takara a babban zabe.

“Ya kamata ‘yan Nijeriya su dauki darasi a kan irin wannan lamari da suka faru a baya. Idan har irin wannan lamari ya taba faruwa a baya kuma kotu ta rushe zaben wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba, lalle kotu tana nan za ta zantar da hukunci a kan wannan mummunan dabi’a.

“Mutanen da suke gudanar da irin wannan lamari suna amfani ne da matsayinsu kuma ya kamata INEC ta yi watsi da irin wannan lamari.

“’Yan takara sun gudanar da zaben fid da gwani kuma har jami’an INEC sun halarci wurin tare da saka ido da amincewa da sunayen wadanda suka samu nasara, sannan bai kamata a sauya sunayen wadanda suka shiga zaben fid da gwani ba da wasu ‘yan takara daban ba,”

Su ma kungiyar lauyoyi sun bayyana cewa lamarin Ahmad Lawan da Godswill Akpabio, a bayana yake na saba wa dokar zabe.

Manyan lauyoyin Nijeriya sun mayar da martani kan sauya sunayen wadanda suka lashe zaben fid da gwani, inda suka suffanta lamarin da take hakkin dokar zabe.

Babban lauya mai suna Kayode Enitan (SAN) ya bayyana cewa INEC ba za ta taba amincewa da sunayen ‘yan takarar da ba su shiga zaben fid da gwani ba, domin ya saba wa sashi na 31 da 33 na dokar zabe.

Ya ce, “Akwai hanyoyin sauya ‘yan takarar da suka lashe zaben fid da gwani kamar yadda sashi na 31 da 33 na dokar zabe ta tanada, ana iya sauya sunayen ne kadai idan dan takara ya mutu.

“Idan dan takarar da ya lashe zaben fid da gwani ya mutu, to dole ne jam’iyya ta sake gudanar da zaben fid da gwani.

“Amma haka kawai, INEC ba ta da hukumin sauya sunayen ‘yan takarar da suka lashe zaben fid da gwani, sai dai dan takara ya janye ko kuma ya mutu.”
Shi ma babban lauya mai suna Matthew Buka (SAN) ya bayyana cewa doka a bayyana take, domin doka ta tanadar da cewa babu wanda zai tsaya takarar babban zabe har sai ya lashe zaben fid da gwani a karkashin jam’iyyun siyasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Malamai Sun Yaba Wa Sarkin Sha’iran Kano Kan Yi Wa Ma’aiki Wakoki 2,000

Next Post

Ci Gaba Abu Ne Na Zahiri A Tarihin Sin

Related

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako
Labarai

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

7 hours ago
EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80
Labarai

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

9 hours ago
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5
Manyan Labarai

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

15 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 

15 hours ago
Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya
Labaran Kasuwanci

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

16 hours ago
Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa
Labarai

Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa

18 hours ago
Next Post
Ci Gaba Abu Ne Na Zahiri A Tarihin Sin

Ci Gaba Abu Ne Na Zahiri A Tarihin Sin

LABARAI MASU NASABA

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

June 21, 2025
CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

June 21, 2025
Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

June 21, 2025
EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

June 21, 2025
Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

June 21, 2025
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

June 21, 2025
Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

June 21, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran

Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran

June 21, 2025
Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

June 21, 2025
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

June 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.