• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Lauyoyi Sun Murza Gashin Baki Kan Sauya Halattattun ‘Yan Takara Da Wasu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Lauyoyi

Lauyoyi da Kungiyoyin Fararen Hula sun murza gashin baki a kan cewa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta yi watsi da duk wani dan takarar da bai shiga zaben fid da gwani ba da jam’iyyun siyasa suka tura mata sunayensu.

Gamayyar kungiyoyin fararen hula sun zargi jam’iyyun siyasa da tura wa INEC da sunayen wasu ‘yan takara wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba a matsayin ‘yan takararsu tare da cire sunayen ‘yan takarar da suka lashe zaben fitar da gwani.

Binciken LEADERSHIP ya gano cewa jam’iyyar APC ta tura wa INEC sunayen manyen ‘yan siyasa wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba a matsayin ‘yan takararsu.

Gamayyar kungiyoyin sun siffanta lamarin da rashin adalci tare da bayyana cewa dole jam’iyyun siyasan su fuskanci hukunci domin kuwa kotu ta shirya tsaf wajen yakar irin wannan gurbatacciyar dimokuradiyya.

Da yake zantawa da LEADERSHIP, shugaban gamayyar kungiyoyin fararen huda, Awwal Musa Rafsanjani ya bayyana cewa bai kamata a bar ‘yan siyasa suna yin abin da suka ga dama ba. Ya kara da cewa su ne manyan wadanda suka fi amfana da dimokuradiyya kuma ne suke lalata ta.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Ya ce, “Wannan wasu dabi’u ne da gurbatattun ‘yan siyasa ke yi kuma INEC tana kara musu kwarin gwiwa a wajen gudanar da zaben fid da gwani, saboda ta yaya wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba a ba su damar tsayawa takara a babban zabe.

“Ya kamata ‘yan Nijeriya su dauki darasi a kan irin wannan lamari da suka faru a baya. Idan har irin wannan lamari ya taba faruwa a baya kuma kotu ta rushe zaben wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba, lalle kotu tana nan za ta zantar da hukunci a kan wannan mummunan dabi’a.

“Mutanen da suke gudanar da irin wannan lamari suna amfani ne da matsayinsu kuma ya kamata INEC ta yi watsi da irin wannan lamari.

“’Yan takara sun gudanar da zaben fid da gwani kuma har jami’an INEC sun halarci wurin tare da saka ido da amincewa da sunayen wadanda suka samu nasara, sannan bai kamata a sauya sunayen wadanda suka shiga zaben fid da gwani ba da wasu ‘yan takara daban ba,”

Su ma kungiyar lauyoyi sun bayyana cewa lamarin Ahmad Lawan da Godswill Akpabio, a bayana yake na saba wa dokar zabe.

Manyan lauyoyin Nijeriya sun mayar da martani kan sauya sunayen wadanda suka lashe zaben fid da gwani, inda suka suffanta lamarin da take hakkin dokar zabe.

Babban lauya mai suna Kayode Enitan (SAN) ya bayyana cewa INEC ba za ta taba amincewa da sunayen ‘yan takarar da ba su shiga zaben fid da gwani ba, domin ya saba wa sashi na 31 da 33 na dokar zabe.

Ya ce, “Akwai hanyoyin sauya ‘yan takarar da suka lashe zaben fid da gwani kamar yadda sashi na 31 da 33 na dokar zabe ta tanada, ana iya sauya sunayen ne kadai idan dan takara ya mutu.

“Idan dan takarar da ya lashe zaben fid da gwani ya mutu, to dole ne jam’iyya ta sake gudanar da zaben fid da gwani.

“Amma haka kawai, INEC ba ta da hukumin sauya sunayen ‘yan takarar da suka lashe zaben fid da gwani, sai dai dan takara ya janye ko kuma ya mutu.”
Shi ma babban lauya mai suna Matthew Buka (SAN) ya bayyana cewa doka a bayyana take, domin doka ta tanadar da cewa babu wanda zai tsaya takarar babban zabe har sai ya lashe zaben fid da gwani a karkashin jam’iyyun siyasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC
Manyan Labarai

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
Kotu Da Ɗansanda

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
Next Post
Ci Gaba Abu Ne Na Zahiri A Tarihin Sin

Ci Gaba Abu Ne Na Zahiri A Tarihin Sin

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.