• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Lauyoyi Sun Murza Gashin Baki Kan Sauya Halattattun ‘Yan Takara Da Wasu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
Dalilinmu Na Karbar Sunan Ahmed Lawan Maimakon Na Machina – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Lauyoyi da Kungiyoyin Fararen Hula sun murza gashin baki a kan cewa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta yi watsi da duk wani dan takarar da bai shiga zaben fid da gwani ba da jam’iyyun siyasa suka tura mata sunayensu.

Gamayyar kungiyoyin fararen hula sun zargi jam’iyyun siyasa da tura wa INEC da sunayen wasu ‘yan takara wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba a matsayin ‘yan takararsu tare da cire sunayen ‘yan takarar da suka lashe zaben fitar da gwani.

Binciken LEADERSHIP ya gano cewa jam’iyyar APC ta tura wa INEC sunayen manyen ‘yan siyasa wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba a matsayin ‘yan takararsu.

Gamayyar kungiyoyin sun siffanta lamarin da rashin adalci tare da bayyana cewa dole jam’iyyun siyasan su fuskanci hukunci domin kuwa kotu ta shirya tsaf wajen yakar irin wannan gurbatacciyar dimokuradiyya.

Da yake zantawa da LEADERSHIP, shugaban gamayyar kungiyoyin fararen huda, Awwal Musa Rafsanjani ya bayyana cewa bai kamata a bar ‘yan siyasa suna yin abin da suka ga dama ba. Ya kara da cewa su ne manyan wadanda suka fi amfana da dimokuradiyya kuma ne suke lalata ta.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Ya ce, “Wannan wasu dabi’u ne da gurbatattun ‘yan siyasa ke yi kuma INEC tana kara musu kwarin gwiwa a wajen gudanar da zaben fid da gwani, saboda ta yaya wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba a ba su damar tsayawa takara a babban zabe.

“Ya kamata ‘yan Nijeriya su dauki darasi a kan irin wannan lamari da suka faru a baya. Idan har irin wannan lamari ya taba faruwa a baya kuma kotu ta rushe zaben wadanda ba su shiga zaben fid da gwani ba, lalle kotu tana nan za ta zantar da hukunci a kan wannan mummunan dabi’a.

“Mutanen da suke gudanar da irin wannan lamari suna amfani ne da matsayinsu kuma ya kamata INEC ta yi watsi da irin wannan lamari.

“’Yan takara sun gudanar da zaben fid da gwani kuma har jami’an INEC sun halarci wurin tare da saka ido da amincewa da sunayen wadanda suka samu nasara, sannan bai kamata a sauya sunayen wadanda suka shiga zaben fid da gwani ba da wasu ‘yan takara daban ba,”

Su ma kungiyar lauyoyi sun bayyana cewa lamarin Ahmad Lawan da Godswill Akpabio, a bayana yake na saba wa dokar zabe.

Manyan lauyoyin Nijeriya sun mayar da martani kan sauya sunayen wadanda suka lashe zaben fid da gwani, inda suka suffanta lamarin da take hakkin dokar zabe.

Babban lauya mai suna Kayode Enitan (SAN) ya bayyana cewa INEC ba za ta taba amincewa da sunayen ‘yan takarar da ba su shiga zaben fid da gwani ba, domin ya saba wa sashi na 31 da 33 na dokar zabe.

Ya ce, “Akwai hanyoyin sauya ‘yan takarar da suka lashe zaben fid da gwani kamar yadda sashi na 31 da 33 na dokar zabe ta tanada, ana iya sauya sunayen ne kadai idan dan takara ya mutu.

“Idan dan takarar da ya lashe zaben fid da gwani ya mutu, to dole ne jam’iyya ta sake gudanar da zaben fid da gwani.

“Amma haka kawai, INEC ba ta da hukumin sauya sunayen ‘yan takarar da suka lashe zaben fid da gwani, sai dai dan takara ya janye ko kuma ya mutu.”
Shi ma babban lauya mai suna Matthew Buka (SAN) ya bayyana cewa doka a bayyana take, domin doka ta tanadar da cewa babu wanda zai tsaya takarar babban zabe har sai ya lashe zaben fid da gwani a karkashin jam’iyyun siyasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Malamai Sun Yaba Wa Sarkin Sha’iran Kano Kan Yi Wa Ma’aiki Wakoki 2,000

Next Post

Ci Gaba Abu Ne Na Zahiri A Tarihin Sin

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

7 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

8 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

10 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

13 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

15 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

16 hours ago
Next Post
Ci Gaba Abu Ne Na Zahiri A Tarihin Sin

Ci Gaba Abu Ne Na Zahiri A Tarihin Sin

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.