• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

by Sani Anwar
2 hours ago
in Rahotonni
0
2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da zaben 2027 ke kara karatowa, jam’iyyun siyasa Nijeriya na dakon jiran ganin sabon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), wanda suka kara jaddada muhimmancin samun sahihin zabe da rashin son zuciya da sadaukarwa ga ka’idojin dimokuradiyya.

A cikin wata tattaunawa ta musamman da manema labarai, APC ta bukaci sabon shugaban INEC da ya tabbatar da cewa kowacce jam’iyyar siyasa ta samu martaba daidai ga dukkan jam’iyyun Nijeriya, yayin da PDP ta jaddada bukatar shugaban hukumar ya kasance mai zaman kansa da kuma cin gashin kansa.

  • Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace
  • Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa

A gefe guda kuma, ADC ta gargadi cewa rashin gudanar da zabe mai inganci a karkashin sabon shugaban INEC na iya zama barazana ga zaman lafiyar dimokuradiyya a kasar nan.

Shugaban INEC na yanzu, Farfesa Mahmood Yakubu, yana shirin kammala wa’adinsa na biyu kafin watan Nuwamba.

An nada shi a 2015, kuma an sake kara masa wa’adi na biyu a 2020, Yakubu yana da daya daga cikin shugabanin INEC da suka fi dadewa a tarihin hukumar zaben Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Bisa sashe na 154 (1) na kundin tsarin mulkin na 1999 da aka yi wa kwaskwarima, ” shugaban kasa ne zai nada shugaban INEC da mambobin hukumar zabe ta kasa, sannan majalisar dattawa ta tabbatar da su.”

Dangane da tanadin da ke cikin tsarin mulki, Shugaban kasa Bola Tinubu ya bayyana cewa ya tanadi jerin sunayen ‘yan takara da za su meye gurbin Yakubu.

Da yake jawabi kan tsammanin jam’iyyar APC mai mulki, daraktan yada labarai, Bala Ibrahim, ya bayyana cewa yayin da jam’iyyar ke nufin lashe duk zabe, tana jaddada bukatar samun yin aldaci ga kowa.

Ibrahim, a cikin wata hira, ya bayyana cewa, “A matsayinmu na jam’iyya, abin da muka sa a gaba shi ne samun nasarar cin zabe mai cike da inganci.”

“Babban burinmu shi ne, yadda za mu karbe iko ta hanyar da za ta ba da riba ga dimokuradiyya ga mutane. burinmu ita ce yadda za mu tsaya takara a zabe kuma a ba mu damar taka ba tare da an dakatar da mu ko an cire mu daga zabe ba.

“Don haka, muna sa ran samun shugaban hukumar zabe wanda zai ba da dama ga kowa, wanda zai ba da damar gudanar da zabe cikin ‘yanci da adalci. Muna bukatar shugaban INEC da zai yi aiki ka doka.”

Sakataren yada labarai jam’iyyar PDP, Debo Ologunagba, ya jaddada cewa dole ne shugaban INEC da zai zo ya zama mutum mai nagarta.

Ologunagba ya kuma kira ga shugaban kasa da masu ruwa da tsaki masu alkakkin zaben shugaban INEC su yi la’akari da halayen ‘yan takarar sosai kuma su tabbatar an nada mutumin da ke da kwarewa.

Ya bayyana cewa, “Shugaban INEC na gaba ya zama wani mutum mai nagarta, ya zama wanda ba zai kasance mai mummunan hali ba, ya zama mai adalci, wanda zai zama mai ‘yanci kuma ya gudanar da hukumar ta wannan hanyar, kamar yadda doka ta tanada. Don haka wannan shi ne abin da muke tsammani.”

Ita kuwa jam’iyyar hadaka, ta bakin sakataren yada labarai na kasa, Bolaji Abdulahi, ta bayyana damuwa kan rikicin bai wa INEC ‘yancin kanta.

Abdullahi ya bayyana cewa sabon shugaban INEC da za a zaba dole ne ya yi aiki don dawo da amincewa ta hanyar tabbatar da gudanar da zabe mai inganci a 2027.

Ya ce, “Abu mafi muhimmanci shi ne, ina tunanin INEC ta sha fama da rikice-rikice na samun amincewa a idon masu kada kuri’a a Nijeriya a cikin shekaru da dama.”

“Sabon shugaban INEC ya kamata ya tabbatar da cewa hukumar ta ci gaba da kasancewa a matakin amincewa. Ka san cewa, tabbatar da tsarin zabe yana karfafa gwiwar kowa, kuma shi ne kawai hanyar da za a tabbatar da kwanciyar hankali a cikin kasar nan.

“Dole ne su tabbatar da nada mtumin da zai kasance tsayayye da kuma jajircewa. Idan aka kasa yin hakan, hakan na iya haifar da shakku a cikin zukatan ‘yan kasa game da ingancin zaben 2027, ko za su kasance masu ‘yanci da adalci kan zaben.

“Don haka, ina tsammanin shekara ta 2027 za ta zama mai muhimmanci ga kowa. A matsayin jam’iyya, muna fatan cewa nadin zai ba da damar ga wanda ya fahimci muhimmancin tarihi na aikin.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Siyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

Next Post

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Related

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 
Rahotonni

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

1 week ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

2 weeks ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

3 weeks ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

3 weeks ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

3 weeks ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

4 weeks ago
Next Post
Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

September 26, 2025
2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

September 26, 2025
Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

September 26, 2025
’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

September 26, 2025
Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

September 26, 2025
A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

September 26, 2025
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

September 26, 2025
Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

September 26, 2025
An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

September 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

September 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.