• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

by Leadership Hausa
11 hours ago
in Siyasa
0
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kafin zaɓen shekara ta 2027, jam’iyyar APC da hadakar jam’iyyar ADC na gwagwarmayar neman samun goyon bayan mutanen arewa da kuma wacce ta fi dacewa wajen kare muradunsu.

Shugaban jam’iyyar ADC na wucin gadi kuma tsohon shugaban majalisar dattawa, daɓid Mark, ya bayyana cewa talauci da rashin tsaro da ƙuncin tattalin arziki su ne matsalolin da suke yi wa a arewa katutu.

Shi ma tsohon sakataren gwamnatin tarayya kuma jago a ADC, Babachir Lawal, ya bayyana cewa arewa ta amince da jam’iyyar ADC ta hanyar gamayyar ƙungiyar tuntuɓa kan harkokin siyasa ta ƙasa, a matsayin jam’iyya daya tilo da ta fi kare muradunta tare da alwashin ƙwace mulki a hannun APC a 2027.

  • 2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku
  • Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Mark da Lawal sun bayyana wannan a ranar Asabar a lokacin taron gamayyar ƙungiyar tuntuɓa kan harkokin siyasa ta arewa karo na uku da aka gudanar a Abuja.

da yake mayar da martini kan batun, daraktan Yada Labarai na APC, Bala Ibrahim, ya yi iƙirarin cewa jam’iyyar mai mulki tana da goyon baya a duk faɗin ƙasar nan, ciki har da arewacin Nijeriya, inda ya bayyana cewa muradin ƴan Nijeriya na samun kariya ƙarƙashin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa

A yanzu haka dai ratotannin sun tabbatar da cewa APC da ADC suna gogayya wajen neman samun goyon bayan mutanen arewa kafin babban zaɓen 2027 ya ƙariso.

A ranar 1 ga Yuli, manyan ƴan adawa da suka hada da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi da dan takarar shugaban ƙasa a APC a 2023, Rotimi Amaechi, da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, sun gabatar da ADC a matsayin hadakar jam’iyyar adawa domin ƙalubalantar Tinubu a 2027.

Shugabannin ADC sun ci gaba da yin ƙoƙari don samun goyon bayan mutanen arewacin Nijeriya da sauran yankuna tun bayan buɗe jam’iyyar.

A taron, Mark ya buƙaci shugabannin arewacin Nijeriya da su daina dabi’ar zargi da kuma amincewa na suna da alhakkin ƙalubalen da yankin ke fuskanta.

Ya ce, “Wannan wata dama ce da kuma girmamawa kasancewa a gabanku yau don magana kan batun halin da muke ciki a yanzu da kuma sauya makomarmu. Ina kira a gare ku mu yi gaggawar samun haɗin kai da ƙarfafa dangantaka a matsayin hanyar magance ƙalubalen da yankinmu ke fuskanta. 

“Arewacin da muka sani ya kasance wata ƙasa ce mai ɗimbin tarihi da albarkatun ma’adinai da ƙasa noma da al’adu masu yawa da kuma ƙarfin tasiri.

“ɗuk da wadannan albarkatu, muna fuskantar ƙalubale masu yawa da suka hada da rashin tsaro da talauci da rikice-rikicen ƙabilanci da addinai da rarrabuwar kai a siyasa da matsalolin zamantakewar da na tattalin arziki. Wadannan ƙalubale ba su faru a dare daya ba kuma ba za su kau ba har sai mun hada kai wajen daukar matakin da ya dace.

“ɗole ne mu yarda da cewa mu ne masu gina matsalolinmu, dole ne mu daina zargin kawunanmu idan muna son samun mafita ɗorewar yankinmu.”

Tsohon shugaban majalisar dattawa ya ƙara bayyana cewa rarrabuwar kawuna ta hana wa arewacin ƙasar nan ci gaba, yayin da halin ko-in-kula da rashin daukan mataki ya ƙara zurfafa rarrabuwar da ta riga ta wanzu.

“ƙalubalen da ke fuskantar arewacin Nijeriya suna da alaƙa da juna. Rashin tsaro yana janyo ficewar masu zuba jari, wanda hakan ke ƙara tsananta talauci. Talauci yana jawo aikata muyagun laifuka. ƙabilanci na rage ƙarfin haɗin kanmu wajen neman kyakkyawan shugabanci. Rugujewar harkokin siyasa na tabbatar da cewa ba za a samu ingantaccen ci gaba a yankinmu. Wannan ba arewar da muka gada ba ne,” in ji ADC.

ɗon dawo da martaban yanki, Mark ya jaddada cewa akwai buƙatar matanen arewa su sake tunani da yin Nazari wajen daukan matakan da suka dace.

Ya kira ga dukkan mutanen arewa su dauki wannan a matsayin babban nauyi na haɓaka haɗin kai wajen inganta yankin maimakon zama a rarrabe.

A nasa ɓangaren, Lawal ya bayyana cewa gamayyyar ƙungiyar tuntuɓa kan harkokin siyasa ta arewa ta amince da ADC a matsayin jam’iyyar da ta iya tunkarar APC a zaɓen 2027.

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya ya ce wakilai daga dukkanin jihohin arewa 19 sun cimma yarjejeniya cewa gwamnatin Shugaba Tinubu ba ta wani yuƙuri wajen magance matsalolin yankin. 

Ya ce masu ruwa da tsaki daga arewacin ƙasar nan sun amince su tashi tsaye su yada saƙonsu wajen samn haɗin kan mutane da cimma matsaya kan zaɓe mai zuwa. 

A martaninsa, daraktan yada labarai na APC ya ce jam’iyyar mai mulki ba ta damu da abin da ake kira da suna hadakar jam’iyya ba.

Ibrahim ya bayyana cewa Shugaba Tinubu na jagorantar gwamnati mai cike da samun goyon bayan dukkan mutanen Nijeriya.

Ya ce, “Jam’iyarmu ta APC, tana samun goyon bayan mutanen arewacin Nijeriya da kuma dukkan sauyan yankunan Nijeriya gaba daya, sai dai wadanda ba su gamsu ba da suka kafa jam’iyyar ADC a yanzu.”

Ya bayyana cewa APC ta jajirce wajen sabunta fata ga ƴan Nijeriya kuma yana nuna tabbacin cewa jam’iyyar za ta ƙara samun nasara a 2027.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2027ADCAPCArewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Next Post

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Related

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili
Siyasa

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

13 hours ago
Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
Siyasa

Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa

21 hours ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Labarai

2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC

2 days ago
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
Siyasa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

3 days ago
Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC
Siyasa

Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC

4 days ago
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

5 days ago
Next Post
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

LABARAI MASU NASABA

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

August 2, 2025
Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

August 2, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.