• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Haɗewar NILEST Da NARICT Barazana Ce Ga Walwala Da Ayyukan Cibiyoyin’

by Sadiq
2 years ago
NILEST

Ƙungiyar masana fasahar fata da na kimiyyar sinadarai ta Nijeriya ta damu matuƙa da haɗewar Cibiyar Fasahar Fata da Kimiyya ta Nijeriya (NILEST) da kuma Cibiyar Bincike Kan kimiyyar Sinadarai (NARICT), inda ta bayyana cewa hakan babbar barazana ce ga jin daɗi da walwalar masu gudanarwa. 

Idan za a iya tunawa batun haɗewar ma’aikatu da hukumomin gwamnati ya zama ruwan dare tun bayan fitar da rahoton Oronsanye game da sauye-sauyen ayyukan gwamnati sama da shekaru goma sha biyu da suka gabata.

  • ‘Yan Bindiga Sun Tarwatsa Kauyuka 10 A Jihar Kaduna
  • Pogba Zai Ɗaukaka Ƙara A Kan Dakatar Da Shi Daga Buga Ƙwallo Na Tsawon Shekaru 4

Ana ɗaukar wannan matakin a matsayin wata dabara da gwamnati ta ɓullo da shi domin rage kuɗaɗen da ƙasa ke kashewa wajen gudanar da ayyukan gwamnati. Sauran dalilan haɗewar sun haɗa da; kawar da tsarin rashin gudanarwa, maimaita ayyuka, kwaikwayo, da sake fasalin ayyukan gwamnati wanda zai inganta yanayin gudanar da ayyuka.

A cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta masana fasahar fata da kimiyyar sinadarai ta Nijeriya ta fitar ɗauke da sa hannun shugaban ƙungiyar na ƙasa, Dr. Julius Putshaka, ya ce ya zama wajibi a yi nazari sosai kan illolin da ke tattare da irin wannan haɗewar na wasu hukumomi.

Sanarwar ta ƙara da cewa: “rashin amincewar ƙungiyar masana fasahar fata da na kimiyyar sinadarai ta Nijeriya dangane da haɗewar waɗannan hukumomi ya samo asali ne daga damuwar da ke tattare da yiwuwar tafka asarar ƙwararrun masana saboda waɗannan cibiyoyi suna da hurumi daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

“A yayin da NILEST ke da alhakin gudanar da bincike tare da horar da ma’aikata a fannin fasahar fata da ƙirgi tare da samar da ɗaliban da za su yi wa masana’antar fata hidima da kuma wasu sassa da dama a wasu hukumomin gwamnati, Cibiyar NARICT a ɗaya ɓangaren kuma tana da alhakin gudanar da bincike a cikin albarkatun ƙasa domin samar da sinadarai da za a yi amfani da su wajen aikace-aikacen masana’antu.

“Dole ne a nanata cewa NILEST ta taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa ɓangarori masu muhimmanci a ɓangaren samar da fata da ƙirgi. Tare da cibiyoyi masu gudanar da ayyuka da kuma wasu da aka faɗaɗa ayyukan, ofisoshin cibiyar sun bazu a duk yankuna shida na siyasa na faɗin ƙasar, kuma ta kasance a matsayin jagora ga ‘yan kasuwa masu sana’ar dogaro da kai a masana’antar.

“Cibiyar ta horar da dubban ‘yan kasuwa da masu sana’o’in hannu a faɗin ƙasar nan tare da haɗin gwiwar ƙungiyoyi daban-daban da gwamnatocin jihohi kuma har yanzu tana samar da ƙarin hanyoyin gudanar da irin waɗannan ayyuka.

“Yana da kyau a lura da irin tasirin da wannan cibiya za ta iya yi wajen samar da arziƙi da kuma musayar kuɗaɗen ƙasashen waje ga ƙasar nan ta hanyar samar da ingantattun fata da ƙirgi da za a iya fitar da su zuwa ƙasashen waje a manyan cibiyoyinta da ke Sakkwato, Kano, da Maiduguri.

Kamar dai yadda Cibiyar Fata da ta shahara a duniya ta Indiya take, NILEST ita ma tana ba da tallafin fasaha ta hanyar horar da darussan kan haɓaka ƙirƙira, yin samfuri tare da samarwa, bayar da shawarwari da tuntuɓa, shirya rahotannin yadda za a gudanar da ayyuka, da kula da inganci, tare da sauran ɗimbin ayyuka daban-daban.”

Hakazalika sun yi nuni da cewa, da irin nasarorin da aka samu da kuma tasirin da aka samu a ɓangarori da dama, haɗakar ka iya isar da saƙon koma baya a tsakanin masu ruwa da tsaki a masana’antar fata, musamman a wannan lokaci da NILEST ke aiwatar da manufofi da shirin gwamnatin tarayya kan harkokin fata da ƙirgi.

“Muna da ja kan cewa haɗewar na iya haifar da ruɗani wajen yanke hukunci, tare da kuma rage karsashi kan wasu batutuwa ko rashin samun daidaito wajen aiwatar da manufofin gwamnati, kawo cikas ga ayyukan da ake da su ko shirye-shirye a cikin masana’antar fata da NILEST ke aiwatarwa”, in ji sanarwar.

Kazalika sanarwar ta ce za a iya kuma samun karkatar ra’ayoyin masu ruwa da tsaki da kuma gurgunta ƙwazo da dabarun ƙwararru. A matsayin su na masu ruwa da tsaki a kan lamuran fata, kungiyar ta ce ta lura da cewa haɗewar waɗannan cibiyoyi, zai iya zama barazana ga masu ruwa da tsaki wanda zai haifar da gazawar cika alƙawuran alfanun da za a samu na irin wannan haɗakar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus
Manyan Labarai

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Next Post
Kano

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Kar-ta-kwana Kan Haramtattun Gine-gine

LABARAI MASU NASABA

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.