• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

by Yusuf Shuaibu
3 days ago
in Labarai
0
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan siyasa da magoya bayansu sun ci gaba da watsi da gargadin da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta kasa (INEC) ta yi na gudanar da yakin neman zaben 2027.

Duk da umarnin da INEC ta bayar, siyasa tana kara yin zafi a tsakanin masu neman takara da magoya bayansu, yayin da suke kara daukar matakai na tallata burikansu da yin sharyi kan zaben 2027. Yanayin siyasa na kara zafafa a daidai lokacin da ya rage saura shekara biyu a yi zabe a Nijeriya.

Manyan ‘yan siyasa sun fara yin bayani da ke bayyana aniyarsu ta tsayawa takara, yayin da suke kuma neman goyon baya ga masu ruwa da tsaki daban-daban.

Musamman a matakin kasa, jam’iyyar APC mai mulki ta amince da Shugaba Bola Tinubu a matsayin dan takarar shugaban kasa guda daya tilo a zaben 2027, bayan samun goyon baya daga manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar, wato kwamitin zartarwa na kasada kuma na yankuna.

A taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar da aka gudanar a ranar 26 ga Fabrairu, 2025, APC ta amince da tazarcen Shugaba Tinubu.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

A wannan rana, shugaban kungiyar gwamnonin APC kuma Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, ya gabatar da kudrin goyon bayan tazarcen Tinubu. Nan take tsohon gwamnan Jihar Edo da kuma dan majalisar dattawa, Sanata Adams Oshiomhole ya amince da kudirin.

Bayan wata uku, kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar APC ya bayyana shugaban kasa Tinubu a matsayin dan takarar daya tilo na shugaban kasa a zaben 2027.

Haka nan a taron kungiyar gwamnonin APC da ‘yan majalisaun tarayya na jam’iyyar sun amince da Shugaba Tinubu a matsayin dan takararsu na shugaban kasa a zaben 2027.

Kazalika, dan takarar shugaban kasar na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, ya tabbatar da niyyarsa na sake tsayawa takarar shugaban kasa a 2027, tare da alkawarin yin wa’adi guda na shekaru hudu idan aka zabe shi.

Obi ya bayyana hakan ne a shafinsa na Tuwita, inda ya amsa tambayoyin daga masu goyon baya a gida Nijeriya da kuma kasashen waje. Tsohon gwamnan Jihar Anambra ya yi alkawarin sake tsayawa takarar shugaban kasa a 2027.

Hak kuma, tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi, ya bayyana niyyarsa ta takarar shugabancin kasa a 2027, yana bayyana kwarin gwiwar cewa zai iya kayar da Shugaba Tinubu a zaben 2027, idan ya samu tikitin tsayawa takarar shugaban kasa a jam’iyyar ADC.

Amaechi, ya bayyana hakan ne a yayin tattaunawa da aka yi da shi a Shafin Tuwita, ya roki jam’iyyar ADC da su ba shi tikitin takarar shugaban kasa, yana mai jaddada cewa shi ya san lagon karya Shugaba Tinubu da jam’iyyarsa ta APC mai mulki.

Wani bidiyon da ake yadawa kwanan nan game da yiwuwar neman takarar shugaban kasa a 2027 na tsohon dan takarar jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar. Masu sharhi da yawa sun fassara wannan bidiyon a matsayin wata alama ta nufin sake fitowa takara. Duk da haka, mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Paul Ibe, ya musanta ikirarin, yana mai cewa bidiyon an dauke shi ne a 2022, kafin zaben fid da gwani na PDP.

A halin yanzu, a yankin arewa ta tsakiyar, kungiyar shugabannin matasa ta goyi bayan shahararren dan kasuwa, Dakta Gbenga Olawepo-Hashim, a matsayin dan takararsu na shugaban kasa a 2027.

Sun bayyana boyon bayan nasu ne a lokacin taron manema labarai a Abuja, wanda kungiyar matasa na arewa tsakiya (YANCP) ta shirya, ta kasance wata kungiya da ke nuna goyon bayan shugabanci ya tsaya a yankin arewa ta tsakiya a 2027.

Sashe na 94(1) na dokar zabe ta 2022, wanda ya ce jam’iyyun siyasa ba za su fara gudanar da yakin neman zabe ba a bainar jama’a har sai kwanaki 150 kafin ranar zabe kuma ba su wuce sa’o’i 24 kafin wannan ranar ba.

Babban sakataren yada labarai na INEC, Rotimi Oyekanmi, ya shaida wa LEADERSHIP cewa rashin dacewa da kuma rashin bin doka ne ga kowace jam’iyya ta siyasa ta fara gudanar da yakin neman zaben 2027 a wannan lokacin, wanda hakan ya saba wa dokar zabe ta 2022.

“Babu wani tanadi na musamman a cikin dokar zabe ta 2022 da ke haramta goyon bayan ‘yan takara a wurin mutane da kungiyoyi wajen zabe.

“A karkashin sashe na 94(1) na dokar zabe ta 2022, jam’iyyun siyasa ba za su fara yakin neman zabe ba har sai ya rage saura kwana 150 kafin ranar zabe kuma za a dakata a kafin awanni 24 kafin wannan rana.

“Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ba ta saki jadawalin ayyukan zaben 2027 ba, wanda zai bayyana lokacin kamfen ga jam’iyyun siyasa a fili. Saboda haka, zai zama saba wa doka ga kowace jam’iyya ta fara yakin neman zaben 2027 a wannan lokaci,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Next Post

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

3 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

4 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

5 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

7 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

9 hours ago
Next Post
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.