• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

by Sulaiman
2 months ago
Kidaya

Kwamishina mai wakiltar jihar Kaduna a Hukumar ƙidaya ta ƙasa, Hajiya Sa’adatu Dogon Bauchi ta kawo ziyara jihar Kaduna domin ganawa da shugabannin Ƙananan Hukumomin jihar 23, tare da masu ruwa da tsaki, a shirin Hukumar na wayar da kan jama’a game da ƙidayar da ke tafe.

 

A lokacin da ta ziyarci Ƙaramar Hukumar Sabon Gari, Hajiya Sa’adatu ta bayar da shawara ga al’umma kan cewa su fito ƙwan su da ƙarƙwata, su tabbatar da an ƙidaya su, domin ta haka ne kawai gwamnti za ta iya wadatar da su da ababen more rayuwa.

  • Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya
  • Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

Haka kuma Kwamishiyar ta jawo hankalin jama’a game da mahimmacin yin rajisista don karbar shaidar yin aure, haihuwa, saki, mutuwa da dai sauran su, wanda ake bayarwa a ofishin Hukumar a duk jihohin ƙasar nan.

 

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Hajiya Sa’ah ta kuma bayyana cewa ita wannan ƙidaya da yin rajistar haihuwa, aure da sauran su, abubuwa ne masu muhimmanci da za su taimaka wa gwamnati ta san yawan su, ta yadda za su sami nasarar ci gaba da lasar romon Dimokraɗiyya mai yawa, musamman a bangaren ilmi, lafiya da dai sauran abubuwan more rayuwa.

 

Daga nan ne ta jinjina wa Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani da cewar jihar Kaduna ce jiha ta farko da gwamnan ta ya yi yunƙurin gabatar da wayar da kan al’ummar sa game da muhimmancin ƙidaya, kuma lallai yana bayar da cikakken goyon bayan sa a kan haka, inda ya ɗauki nauyin hakan a dukkan Ƙananan Hukumomin jihar.

 

A nasa jawabin, Shugaban Ƙaramar Hukumar Sabon Gari, Malam Jamilu Abubakar Albani (ALGON), wanda ya samu wakilcin mataimakin sa, ya bayyana cewa su a shirye suke su bayar da dukkan goyon bayan da ake nema.

 

Ya ce, su tun a baya sun fara wayar ma al’ummar Ƙaramar Hukumar su kai game da manufa da muhimmancin shirin ƙidayar a gare su. Sun shiga lungu da saƙo don wayar ma da al’ummar su kai game da shirin ƙidayar da ke tunkarowa, wanda zai gudana nan ba da jimawa ba.

 

Ɗaya daga cikin Malaman addinai da suka halarci taron ya tabbatar da ƙidayar al’umma a cikin tsarin addinin musulunci, domin shi ne yake bada damar sanin tsatson dukkan ɗan adam da kuma tabbatar da rayuwa cikin tsari.

 

Shi ma a nasa jawabin, wani Shugaba a addinin kirista ya nuna farin cikin sa, sannan kuma nuna yadda zasu wayar ma da mabiyan su kai game da ƙidayar. Ya kuma ƙara da ceawar a koyaushe hukumar ƙidayar suka shirya, su ma a shirye suke wajen ganin an cimma gaci.

 

A looacin da tawagar Kwamishiyar ta isa Ƙaramar Hukumar Soba, Shygaban Ƙaramar Hukumar, Hon. Muhammad Shehu Lawal Molash, ya bayyana jin daɗin sa da wannan shiri na ƙidaya, inda ya nuna cewa za su bayar da duk gudumawa da haɗin kan da ake nema don samun nasarar aikin.

 

Shi kuwa Sarki Haladu, jan hankalin matasa ya yi da su kauce ma duk wata hayaniya, su zama masu natsuwa tun a yanzu wajen wayar ma da al’umma kai har zuwa kammala shirin.

 

Ya zuwa haɗa wannan rahoton dai, Kwamishiniya Hajiya Sa’adatu Dogon Bauchi tana ci gaba da zagawa zuwa sauran Ƙananan Hukumomin jihar don ƙara wayar da kan jama’a game da muhimmancin wannan ƙidaya da ke tafe.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.