ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Gwamnati Ta Kebe Wuraren Kiwo 368 Don Bunkasa Noma

by Abubakar Abba
3 years ago
Kebe

A kwanan baya ne Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanar da aniyar gwamnatinsa ta samar da wuraren kiwo 368 a Jihohi 25.

Wannan yunkurin dai, manoma da dama da ke a cikin kasar nan, sun bayyana hakan a matsayin matakin da ya dace, inda suka sanar da cewa, matakin zai kuma taimaka matuka wajen rage yawan ricikin da ke aukuwa a tsakanin wasu manoma da makiyaya da ke a fadin kasar nan.

  • Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki
  • Kudin Da NNPC Ke Kashewa A Tallafin Mai Ya Wuce Kima – Hamid Ali

Hakan ya sanya wasu daga cikin jihohin kasar, sun bayar da hadin kai domin a cimma wannan nasarar da gwamnatin tarayya ta sa a gaba.

ADVERTISEMENT

Matakin na Buhari ya dauka ya biyo bayan shawarwari ne da wani kwamiti na musamman ya ba shi, wanda ya yi nuni da cewa, samun wuraren kiwo zai taimaka wajen rage rikicin manoma da makiyaya da aka gaza kawo karshen hakan a kasar nan.

Da yake yin tsokaci kan matakin Shugaban kungiyar manoma ta kasa Kabir Ibrahim ya ce idan aka samu irin wanan gagarumin sauyi, ya kamata mutanen kasar nan su yi na’am da shi, musamman ganin cewa, tsarin zai taimaka wajen kara habaka yin noma kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

An Horas Da Masu Kiwon Dabbobi Dabarun Kiwon Zamani

Mataimakin Shugaban Kasa Ya Yaba Da Tsarin Aikin Noma Na Jihar Jigawa

A cewar shugaban, jihohin Arewa da jihohin Kudu duk daya ake, ba abin da ya bambanta kasar sai ra’ayi, kuma bai kamata a bari ra’ayoyi su raba kan kasar ba, inda ya yi nuni da cewa, ya kamata a hade wuri guda a yi wa kasa aiki da zai kawo ci gaba.

Har ila yau, an ruwaito wani dan majalisar gudanarwa ta hukumar tantance ingantaccen iri na kasa Ibrahim Musa ya ce wannan abu ne da ake da shi a kasa tuntuni, kuma in an mayar da shi yanzu yana da kyau.

A cewarsa, wadannan wuraren kiwon dama tun 1948 ake da su har zamanin su marigayi Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato an yi amfani da su a Jihohin kasar.

Ya sanar da cewa, yunkuri ne mai kyau wanda zai taimaka wajen tattara kan makiyaya a wuri guda, domin a tsugunad da su domin ba yadda za a a yi manomi ya rayu babu makiyayi yana mai cewa makiyayi ba zai rayu ba sai da manomi.

Kabiru ya sanar da cewa, yin hakan zai sa a samu abubuwan more rayuwa cikin sauki har a samu kudaden shiga sosai domin zai taimaka wa tattalin arzikin Nijeriya.

Ya bayyana cewa, ya zama wajibi manoma da makiyaya su sani cewa wannan yunkuri shi ne babban abin alheri ga al’umman kasa da kuma jummar da gwamnatin tarayya take da shi a kara bunkasa fannin aikin noma a kasar nan.

Ya ce idan aka samu dama aka kirkiri wannan shiri na Rugga, zai kawo ci gaba sosai na samun tagomashi irin su makarantu da hanyoyin kiwon lafiya da ruwan sha musamman ga makiyaya.

Ya kara da cewa, zai kara samar da hanyoyin samar da da sana’a ga ‘yan Nijeriya, inda ya yi fatan za a gudanar da aikin a cikin fahimta.

Amma abin taikaici, wasu jihar Kudu maso Gabas da Kudu maso Kudu da Kudu maso Yamma, har da wasu a Arewa irin su Jihar Binuwai sun fito fili sun kasance ba su goyin bayan wannan yunkurin na gwamnatin tarayya ba.

samu amfanin gona wanda an jima ba a samu irinsa ba saboda albarkar damina. Duk da matsin rayuwa a Nijeriya a yau, akwai magunguna da sauran muhimman abubuwan rayuwa da mutane za su saya ba kamar a Benezuela ba.

Wannan bambanci tsakanin kasar biyu wajen tasirin faduwar farashin man fetur a kan rayuwar jama’a ya samo asali ne daga yayin da tattalin arzikin Benezuela da mutanen ta suka dogara kacokam a kan man fetur domin samun kudaden shiga da abinci da sauran muhimman abubuwan more rayuwa daga kasashen.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abubuwa Biyar Game Da Kiwon Talotalo
Noma Da Kiwo

An Horas Da Masu Kiwon Dabbobi Dabarun Kiwon Zamani

December 20, 2025
Mataimakin Shugaban Kasa Ya Yaba Da Tsarin Aikin Noma Na Jihar Jigawa
Noma Da Kiwo

Mataimakin Shugaban Kasa Ya Yaba Da Tsarin Aikin Noma Na Jihar Jigawa

December 19, 2025
Kiwon Dabbobi Da Fasahar Kimiyyar Zaman
Noma Da Kiwo

Kiwon Dabbobi Da Fasahar Kimiyyar Zaman

December 14, 2025
Next Post
Wasu Kasashen Da Suka Daddale Yarjejeniyar RCEP Na Fatan Kara Yin Hada-hadar Ba Da Hidimomi Da Kasar Sin

Wasu Kasashen Da Suka Daddale Yarjejeniyar RCEP Na Fatan Kara Yin Hada-hadar Ba Da Hidimomi Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.