ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bola Ta Mamaye Sassan Babban Birnin Tarayya

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
4 weeks ago
Bola

Ba kamar dai yadda abin ya kamata  ya kasance ba wato dattin da ake  ta cin  karo da shi  da kuma  gani a kan tituna ne, shi yasa lamarin yake da matukar  tada hankali ne domin kuwa haka abin yake kasancewa,a  kan tituna, da cikin Kasuwanni, da kuma hanyoyi, saboda wasu  abubuwan da suka hada da rashin  wuraren da ya dace a rika sa shara da kuma rashin kwashewar.Irin wannan matsalar da take gurbatawa da lalata muhalli ko shakka babu abin gaskiya ne domin kuwa sun ce yana matukar taimakawa ga abubwan da sune suke kawo cikas ga lafiyar al’umma da kuma yiyuwar kamuwa ko barkewar cututtuka,wanda daga karshe yana dakushe karkashi da ganin kimar shi Babban Birnin tarayyar.

Mazauna shii Birnin da masu kawo ziyara sun a ci gaba da nuna damuwarsu kan yadda ake zubar da shara da yaduwar Bololi masu yawa kan manyan hanyoy wanda lamarin na rashin kulawa, da maida hankali na wadanda alhakin yin hakan ya rataya a wuyansu domin rashin nuna damuwa ta kawar da ko kwashe su.

Idan mutu ya biyo da ganin yadda manyan garuruwan na Babban Birnin tarayyar suke kamar Wuse, Utako, Garki, Gwarinpa, Jabi, Life Camp da kuma Nyanya, yanzu yawan shara nan da can, ana iya cewa suna gasa ne da irin yadda tsarin mafi dacewa na yadda shi BabbanBirnin ya kamata ya kasance.

ADVERTISEMENT

Ya yin da wari na rubabbun abubuwan da suka lalace iska na dauka warin zuwa sama, yayin da su kuma masu harka da Bola da wasu Dabbobi suke ta harkokinsu a irin wuraren da aka tara Dalar Bola daban- daban inda ya kamata ake zubawa amma kwashewar tana neman gagara kamar yadda ya dace.

Birnin Tarayya da ya zama abin burgewa da sha’awa a lokutan baya, da tunfarko an tsara  shi ne, sai dai kuam yanzu abin ya zama Muhallin ne da ya dace ya rika kasance kowane lokaci abin ban sha’awa, yanzu sai dai wadanda abin ya zama masu dole suke harkokinsu da mazaunan shi ,har ma suke nuna abin tamkar kamar bai damesu ba.

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

“Ko ta in aka duba, za ka lura d akwai yawan shara da aka zuba wurun da aka saba sawa azo a kwashe amma makonni da yawa yin hakan bai samu ba,” kamar dai yadda Oritoke Olalekan, mazaunin Wuse ya nuna rashin jin dadinsa.

“Da alama hukumar kula da kiyaye yadda muhallin Babban Birnin tarayya da kamata ya kasance (AEPB) ta yi dogon Bacci ne da yasa har yanzu bata farka ba.Domin kuwa ai wannan shi ne babban aikinsu layuyyuka su kasance cikin tsafta, sai dai kuma yanzu yin hakan na neman gagararta har ta kai faduwar Tasa.”

 

Masu motoci da ‘yankasuwa suma sun nuna rashin jin dadinsu

Rafiu Jimoh-Adebukola, wani direban tashi da yake yin aiki a Utako, ya ce  ba karamar barazana bane ga abinda ya shafi lafiya da hadarin dake tattare da yi ma abin rikon sakinar Kashi.

“Idan sharer ta taru da yawa, mutane su kan kunna mata wuta domin su rage irin warin da take yi. Hayakin yana rage mana yadda muke kallon abubuwa sosai da kuma sa numfashinmu ya zama mai wahala. Wani lokaci ma ‘Bata- Gari’ su kan boye irin wuraren da ake tara sharer da yawa su rika kwayyce wayoyin mutane bama kamar idan, an samu cinkoson motoci  kamar yadda ya jaddada,”.

A kwanar zuwa Life Camp kuma mahadar Nyanya, mazauna wurin sun ce yawan wuraren da ke tara shara ya zama tamkar wani wuri ne na dindindin domin tara sharar. Wuraren su kan j ara’ayi masu mu’amala da kome yawan sharer da aka tara,wadanda aka fi sani da suna “Baban bola,” wadanda suke daukar wasu kayan da za a iya sake yin amfani da su idan aka yi wata dabara  ko amfani da fasaha,amma sau da yawa su kan yawancin abubuwan da basu kamata su barai ba a wurin.

Irin hakan kamar yadda su mazauna wuraren / garuruwan suka bayyana yana taimakawa masu aikata laifuka wajen jindadinsu yadda za su aikata abubuwan da suke yi.

“Suk ace sun wuraren da irin su masu mu;amalar da sharar ake samun matsala da su ta yin sata ko aikata abubuwan da babu dadin ji. Bayan an kama su ‘yansanda na sakinsu bayan sun amshi cin- hanci,” kamar yadda Taye Ayedero yayi zargin hakan na faruwa, wani direba shi ma, cewa ya yi sun gaji da kai wa gwamnati kuka,“;kamata ya yi ita gwamnatin ta daukai mataki.

Lamarin hakanan yake a Wuye, Garki da kuma wasu wurare d a kuma gundumar Maitama.

Wata mazauniyar Wuye, Esther Ishaya cewa ta yi abin yana kara kasancewa wata babbar matsala, inda tace sharar da aka tara wurin ta dade har wata uku ko fiye da haka.

 

Lamarin ya fi baci a Gwarinpa

Masu harkokin kasuwanci da masu hada- hadar motoci a kusa da  gundumar Gwarinpa suma suna nuna rashiin jin dadinsu kan yadda wuraren da ake tara ko zuba shara ya zama wani abin  damuwa kan wasu manyan hanyoyi a gundumar.

Wuraren da abin ya fi muni sun hada da wadand a suke kan hanyar 3rd Abenue Road, ta shiga wuraren kwana na ayyuka da gidaje, har ma da kusa da kasuwar Kado-Bimko market.

Yayin da masu harkokin kasuwanci suke  nuna rashin jin dadinsu na abubuwan da ke sa wuraren nasu wurin ba wanda za a zauna bane har ayi tunanin yin wata harka  musamman ma abokan huldarsu na kasuwanci,masu harkar tuki suma abin yana ci masu Tuwo a kwarya, domin kuwa shara ta rufe hanya, abinda ke kawo cunkoson abubuwan hawa musamman ma lokacin da aka taso daga aiki.

Daya daga cikin masu shaguna da aka tattauna da shi, Fidelis Oketa, ya ce akwai wani “abu mai tada zuciya da yake fitowa daga cikin tarin sharar wanda ba karamar guba bace tana kuma samar da illa ga lafiyar dan Adam’’.

 

“Mun kai kukanmu ga hukumar gidaje ta gwamnatin tarayya ba sau daya ko biyu ba, domin sune suke bada fili ga duk wanda aka gani nan,amma duk abin ba wani matakin da suka dauka .A matsayi na mai wanda ke harkokin kasuwanci na zuba milyoyin Nairori, ya kuma kasance ina fuskantar irin hakan ai abin wani ci baya ne. Duk yawancin abokan hulda ta sun guje mani ba su zuwa wuri na yanzu saboda irin halin da muke fuskanta yanzu.”

Shi ma da yake magana wata mai gidan abinci kusa da cibiyar, Blessing Daniel,ta ce ta rasa fiye da kashi 70 na masu zuwa su sayi abinci wurinta amma yanzu basu zuwa saboda halin da wurin yake ciki.

“Sabbin fuskokin da su kan zo nan, sai ta kasance ta kyar suke iya tsayawa su kare cin abincinsu, suna barin wurin ne ba tare bata lokaci ba, sauri- sauri suke yi, maimakon su ce a kara sa masu wani abincin lokacin da suke cikin ci.”

Mai harkar abincin sayarwa ta ce wadanda suke lura da kwashe sharar saboda yana da matukar wuya ba duka bane suke kwashe shara koda kuwa sun zo din.

“Za su zo wurin kwashe sharar sau biyu daganan sai su  bar wurin zuwa wani wuri kamar yadda ta ce,”.

Ta bada shawarar a maida wurin da ake zubar da sharar zuwa wani wuri da yafi dacewa da a rika kai sharar.

Wani direban Tasi da yake harkar  tuki, Jamilu Sulaiman, ya ce masu motoci suna fuskantar matsala ta yin zirga- zurga a wuraren kamar yadda suke son yi,  domin kuwa wasu hanyoyin yawan tarin sharar da aka zuba ya rufe su.

Wani shugaban al’umma, Malam Abubakar Ali,  ya yi kira da hukumar kare muhalli ta Babban Birnin tarayya wato AEPB ta shigo cikin lamarin ,  domin kuwa duk irin kokarin da mazauna wurin suka yi bai yi wani tasiri ba.

Shugaban al’ummar Kado-Bimko, Malam Ibrahim Isiaku, wanda shi ma wurin na shi an lalata shi wuraren da aka zuba ko tara shara,  ya ce bayanin da suka samu daga wurin hukumar shi ne  kwangilar da aka bada ta kwashe shara a wurin ta kare ta  dade da karewa.

Ya ce saboda haka ne, wasu mazauna wurin ne suka yanke shawarar sune za su rika biyan kudaden da za’a kwashe masu shara, ta hanayar masu shaguna da kuma sauran masu harkokin kasuwanci a wurin.

Za a iya samun matsalar  barkewar annobar da za ta shafi lafiyar al’umma

Kwararre  bangaren lafiyar al’umma ya ja kunne wadanda ke da ruwa da tsaki cewa matsalolin da za ‘a iya fuskanta dnaganta da rashin kwashe rana abin  duk yafi wani tunanin da mutum zai yi.Kamar yadda suka yi bayani , sharar da ta fara yin wari tana samar da wasu sinadarai masu cutarwa kamar su methane da ammonia, wadada za su iya sanadiyar samar da cututtukan da suke da alaka da lamarin daya shafi numfashi da sauran wasu cututtuka.

Daga Daily Trust muka samo wannan mukalar

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace
Rahotonni

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025
Tinubu Ya Nuna Kwarewa Da Gogewa A Sha’anin Mulkin Nijeriya – Bishir Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Nuna Kwarewa Da Gogewa A Sha’anin Mulkin Nijeriya – Bishir Dauda

December 19, 2025
Next Post
Majalisar Dattawa Ta Bukaci Tinubu Ya Dauki Sojoji 100,000

Majalisar Dattawa Ta Bukaci Tinubu Ya Dauki Sojoji 100,000

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.