ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Bukaci Tinubu Ya Dauki Sojoji 100,000

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
10 months ago
Sojoji

Majalisar Dattijai a ranar Talata ta nuna sabuwar damuwa kan tabarbarewar yanayin tsaro a kasar sannan ta yi kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta amincewa da daukar akalla matasa 100,000 cikin rundunar sojoji domin karfafa tsarin tsaro na Nijeriya da ya gajiya.

‘Yan majalisar sun kuma yanke shawarar kafa kwamitin musamman domin bincikar yadda aka yi amfani da kudaden da aka ware shekaru da dama don Shirin Makarantu Masu Tsaro (Safe School Programme), a yayin da ake sake nuna damuwa cewa makarantun Nijeriya na ci gaba da kasancewa cikin hadari, inda a baya-bayan nan aka sace ‘yan mata a Jihar Kebbi.

  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Matar Sarkin Suleja Mai Martaba Malam Muhammad Awwal Ibrahim Ta Rasu

Wadannan kuduri sun biyo bayan tayin da Sanata Abdullahi Yahaya (APC, Kebbi North) ya gabatar, wanda ya yi gargadi cewa tsaro ya kai matakin tashin hankali wanda ke bukatar gaggawa da matakin kasa mai karfi.

ADVERTISEMENT

A yayin tattaunawa, Sanata Abdul Ningi (PDP, Bauchi Central) ya bayyana yanayin a matsayin “barazana mai tsanani ga rayuwar kasa”, yana rokon abokan aikinsa da su tabbatar da abin domin magance matsalar.

Tinubu Ya Shaida Wa Duke na Edinburgh Cewa Gyare-gyarenmu Zai Karfafa Matasa Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

“Ba za mu siyasantar da wannan lamari ba domin wadannan yara ba namu bane,” in ji shi.

Sanata Aminu Tambuwal (PDP, Sokoto South) ya ce kasar ta fada cikin tarkon abokan gaba, yana gargadin cewa gazawar haduwa don yaki da rashin tsaro zai iya barazana ga makomar Nijeriya.

Tsohon Shugaban Majalisar Dattijai, Ahmad Lawan (APC, Yobe North), ya nuna damuwa cewa duk da manyan kasafin kudi da aka ware ga bangaren tsaro, hare-hare da kisan kai na ci gaba da faruwa.

“Wadannan yara ne shugabannin gobe. Dole mu yi duk mai yiwuwa domin kare su,” in ji shi.

Sanata Orji Uzor Kalu (APC, Abia North) ya zargi gwamnonin jihohi da watsi da rawar da kundin tsarin mulki ya basu a harkar tsaro.

“Tsaro ba nauyin gwamnatin tarayya kadai bane. Dole ne a shigar da gwamnonin jihohi,” in ji shi, yana kara da cewa a lokacin mulkinsa a matsayin gwamnan Abia, ya kaddamar da wannan kalubale.

Sanata Bictor Umeh (LP, Anambra Central) ya yi kira ga amfani da fasahar zamani wajen tattara bayanan leken asiri domin gano da ceto yaran da aka sace, yayin da Sanata Simon Lalong (APC, Plateau South) ya tambayi dalilin da ya sa ’yanmatan makaranta ke ci gaba da zama makasudin hare-hare.

“In an ce yarinyar ta aikata laifi a ina? Shin muna cewa ba ma son ’yanmata su je makaranta? Wannan gaggawa ce ta kasa baki daya,” in ji shi.

Majalisar Dattijai ta amince da karin tayin da Sanata Adams Oshiomhole (APC, Edo North) ya gabatar, wanda ke nema a dauki matasa 100,000 cikin rundunar sojoji.

Oshiomhole ya jaddada cewa sabbin dauka dole ne a horar da su sosai kuma a ba su kayan aiki domin tunkarar ’yan bindiga, ’yan ta’adda, da sauran kungiyoyin tashin hankali da ke harzuka da kasa.

Majalisar Dattijai ta kuma goyi bayan kara amfani da fasahar leken asiri da na’ura mai hangen nesa na zamani domin yakar rashin tsaro da taimakawa wajen gano ‘yanmatan makaranta da aka sace a Jihar Kebbi.

Sojoji
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
Sojoji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post

Adadin Ɗaliban Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja Ya Kai 315 - CAN

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.