ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Za Ta Taimaka Wa Nijeriya Da Bayanan Leƙen Asiri Da Kayan Yaƙi – Fadar Shugaban Ƙasa

by Sadiq
4 weeks ago
Amurka

Gwamnatin Tarayya ta ce Amurka ta amince za ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwarta wajen tsaron Nijeriya.

Wannan ya haɗa da ba da ƙarin bayanan leƙen asiri da kayan tsaro don taimaka wa yaƙi da ’yan ta’adda da ƙungiyoyin da ke haddasa rikici.

  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Goyon Baya Ga Sake Bincikar Laifukan Da Japan Ta Tafka
  • Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Wasanni 8 Da Ta Buga

Wannan mataki ya biyo bayan taruka da aka yi a Washington, DC, tsakanin manyan jami’an Nijeriya da hukumomin gwamnatin Amurka.

ADVERTISEMENT

Tawagar Nijeriya ƙarƙashin jagorancin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Sha’anin Tsaro, Nuhu Ribadu, ta haɗa da Babban Lauyan Ƙasa, hafsoshin tsaro, da Sufeto Janar na ’Yansanda.

A yayin tattaunawar, tawagar Nijeriya ta ƙaryata zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Sun ce rikicin da ke faruwa yana shafar al’ummomi daban-daban ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba, kuma kiran shi da kisan ƙare dangi ba daidai ba ne.

Ƙasashen biyu sun amince su fara aiwatar da sabuwar yarjejeniyar haɗin gwiwa nan take, tare da kafa kwamitin haɗin gwiwa domin tsara aikin tsaro tare.

Amurka kuma ta yi alƙawarin bayar da agajin jin-ƙai da taimako wajen inganta tsarin gano barazana tun wuri.

Gwamnatin Nijeriya ta ƙara tabbatar da ƙudirinta na kare fararen hula da kuma tabbatar da ’yancin addini.

Wannan tattaunawar na zuwa ne biyo bayan barazanar Shugaban Amurka Donald Trump, wanda ya yi iƙirarin cewa ana kashe Kiristoci a Nijeriya.

Shugaba Bola Tinubu ya musanta wannan zargi, yana mai cewa Nijeriya ƙasa ce da ake zaman lafiya da yarda da juna a tsakanin addinai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Gwamnonin Kudu Maso Yamma Sun Sake Jaddada Buƙatar Kafa ’Yansandan Jihohi

Gwamnonin Kudu Maso Yamma Sun Sake Jaddada Buƙatar Kafa ’Yansandan Jihohi

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.