ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Za Ta Taimaka Wa Nijeriya Da Bayanan Leƙen Asiri Da Kayan Yaƙi – Fadar Shugaban Ƙasa

by Sadiq
8 months ago
Amurka

Gwamnatin Tarayya ta ce Amurka ta amince za ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwarta wajen tsaron Nijeriya.

Wannan ya haɗa da ba da ƙarin bayanan leƙen asiri da kayan tsaro don taimaka wa yaƙi da ’yan ta’adda da ƙungiyoyin da ke haddasa rikici.

  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Goyon Baya Ga Sake Bincikar Laifukan Da Japan Ta Tafka
  • Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Wasanni 8 Da Ta Buga

Wannan mataki ya biyo bayan taruka da aka yi a Washington, DC, tsakanin manyan jami’an Nijeriya da hukumomin gwamnatin Amurka.

ADVERTISEMENT

Tawagar Nijeriya ƙarƙashin jagorancin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Sha’anin Tsaro, Nuhu Ribadu, ta haɗa da Babban Lauyan Ƙasa, hafsoshin tsaro, da Sufeto Janar na ’Yansanda.

A yayin tattaunawar, tawagar Nijeriya ta ƙaryata zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.

LABARAI MASU NASABA

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Sun ce rikicin da ke faruwa yana shafar al’ummomi daban-daban ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba, kuma kiran shi da kisan ƙare dangi ba daidai ba ne.

Ƙasashen biyu sun amince su fara aiwatar da sabuwar yarjejeniyar haɗin gwiwa nan take, tare da kafa kwamitin haɗin gwiwa domin tsara aikin tsaro tare.

Amurka kuma ta yi alƙawarin bayar da agajin jin-ƙai da taimako wajen inganta tsarin gano barazana tun wuri.

Gwamnatin Nijeriya ta ƙara tabbatar da ƙudirinta na kare fararen hula da kuma tabbatar da ’yancin addini.

Wannan tattaunawar na zuwa ne biyo bayan barazanar Shugaban Amurka Donald Trump, wanda ya yi iƙirarin cewa ana kashe Kiristoci a Nijeriya.

Shugaba Bola Tinubu ya musanta wannan zargi, yana mai cewa Nijeriya ƙasa ce da ake zaman lafiya da yarda da juna a tsakanin addinai.

MASU ALAKA

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya
Manyan Labarai

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 24, 2026
Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC
Manyan Labarai

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
Next Post
Gwamnonin Kudu Maso Yamma Sun Sake Jaddada Buƙatar Kafa ’Yansandan Jihohi

Gwamnonin Kudu Maso Yamma Sun Sake Jaddada Buƙatar Kafa ’Yansandan Jihohi

LABARAI MASU NASABA

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

July 24, 2026
Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

July 24, 2026
Yadda ‘Yan Spain Suka Mamaye Kyaututtukan Kofin Duniya

Yadda ‘Yan Spain Suka Mamaye Kyaututtukan Kofin Duniya

July 24, 2026
Amurka

Wasiƙar Trump Ba Za Ta Ceto Tinubu Daga Faduwa Zaɓe Ba – Jam’iyyar ADC

July 24, 2026
Falalar Yawaita Istigifari (2)

Falalar Yawaita Istigifari (2)

July 24, 2026
Amurka

Amurka Ta Kakaba Harajin Kaso 12.5% A Kan kayayyakin Nijeriya

July 24, 2026
Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

July 24, 2026
Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

July 24, 2026
NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

July 24, 2026
Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.