ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron G20: Afirka Tana Da Wata Abokiyar Gaske

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 weeks ago
G20

Wace ce abokiyar gaske ta nahiyar Afirka? Kasar Sin ce.

Taron kolin G20 da ya gudana a kasar Afrika ta Kudu a kwanan nan ya tabbatar da hakan.

To, ta yaya za a bambanta abokai na gaske, da wadanda ba su da gaskiya?

ADVERTISEMENT

Da farko, duba ko za su mai da hankali kan moriyarka.

A lokacin taron kolin G20 na wannan karo, kasar Sin da kasar Afirka ta Kudu sun gabatar da shawarar yin hadin gwiwa don zamanantar da nahiyar Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?

Me Ya Sa Aka Kayyade Yin Amfani Da Sinadaran Narkar Da Kankara A Beijing

A cikin shawarar, an lura da bukatar kasashen Afirka ta zamanantarwa, kana an tsara wasu ka’idoji kan hadin gwiwar da ake yi don neman zamanantar da Afirka, wadanda suka hada da tabbatar da adalci, da amfanawa juna, da kula da moriyar jama’a, da kare mabambantan al’adu, da inganta muhallin halittu, gami da samar da tsaro.

Idan an yi hadin gwiwa a duniya, bisa wadannan ka’idoji, to, za a iya tabbatar da babbar moriyar kasashen Afirka.

A zahiri, sai wata abokiyar gaske ce za ta iya gabatar da wannan shawara.

Na biyu kuma, sai a kwatanta matakan da mabambantan bangarori suka dauka.

Daniel Makokera, wani shahararren marubuci dan kasar Afirka ta Kudu, ya rubuta wani bayani a shafin yanar gizo na allAfrica a kwanan nan, inda ya kwatanta matakan kasar Sin da na kasar Amurka, dangane da Afirka.

A cewarsa, kasar Sin tana zuba jari don raya tattalin arzikin Afirka, inda take gina layin dogo, da na’urorin samar da wutar lantarki, da tashoshin jiragen ruwa, da yankunan masana’antu, da samar da ilimin sana’a, da fasahohin zamani, gami da daukar matakan soke harajin kwastam, da kare lafiyar jikin manoma ‘yan Afirka, da dai sauransu.

Yayin da kasar Amurka, a nata bangare, manufarta ta kan zama shiri da magana kawai, inda maganar ta kan sauya tsakanin gargadi game da “tarkon bashi”, da suka kan yadda ake gudanar da mulki a kasashen Afirka.

Lokacin da kasar Afirka ta Kudu ta karbi bakuncin taron kolin G20 na wannan karo, kana daukacin nahiyar Afirka ke alfahari da lamarin, kasar Amurka ta ce wai ana wa fararen fata “kisan kare dangi” a kasar Afirka ta Kudu, don haka ta ki tura manyan jami’anta su halarci taron.

A cewar mista Makokera, Amurka tana yin biris da nahiyar Afirka da gangan, don bata son ganin yaduwar ra’ayin cudanyar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da tasowar nahiyar Afirka.

Ko da yake kasar Sin tana kallon nahiyar Afirka a matsayin babbar abokiya mai muhimmanci, kasar Amurka na ci gaba da neman hana kasashen Afirka shiga cibiyar dandalin harkokin siyasa na duniya.

Mista Makokera ya kara da cewa, sakon kasar Sin ga kasashen Afirka shi ne, “ Za mu yi kokari tare don tabbatar da makoma mai haske, amma ba zan taba tilasta muku bin wata turbar raya tattalin arziki ba.” Wannan shi ne abin da ya kamata aboki mai gaskiya ya yi.

Abokantaka ta gaske dake tsakanin Afirka da Sin za ta haifar da wani sabon tsarin duniya, in ji Makokera.

A nan gaba, za mu kara fahimtar muhimmancin taron G20 na wannan karo, saboda ta ba da damar bambanta abokin gaske da wanda ba na gaske ba, da kuma nuna yanayin huldar dake tsakanin Afirka da Sin, da zai zama mai karin inganci a nan gaba. (Bello Wang)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?

December 17, 2025
Me Ya Sa Aka Kayyade Yin Amfani Da Sinadaran Narkar Da Kankara A Beijing
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Kayyade Yin Amfani Da Sinadaran Narkar Da Kankara A Beijing

December 16, 2025
Waiwaye Adon Tafiya : Tasirin Sin A Kan Afirka Ta Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Waiwaye Adon Tafiya : Tasirin Sin A Kan Afirka Ta Fannin Fasahar AI

December 15, 2025
Next Post
Karin Kasashe Masu Tasowa Sun Shiga Aikin Sarrafa Harkokin Tattalin Arzikin Duniya

Karin Kasashe Masu Tasowa Sun Shiga Aikin Sarrafa Harkokin Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.