ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron G20: Afirka Tana Da Wata Abokiyar Gaske

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
G20

Wace ce abokiyar gaske ta nahiyar Afirka? Kasar Sin ce.

Taron kolin G20 da ya gudana a kasar Afrika ta Kudu a kwanan nan ya tabbatar da hakan.

To, ta yaya za a bambanta abokai na gaske, da wadanda ba su da gaskiya?

ADVERTISEMENT

Da farko, duba ko za su mai da hankali kan moriyarka.

A lokacin taron kolin G20 na wannan karo, kasar Sin da kasar Afirka ta Kudu sun gabatar da shawarar yin hadin gwiwa don zamanantar da nahiyar Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

A cikin shawarar, an lura da bukatar kasashen Afirka ta zamanantarwa, kana an tsara wasu ka’idoji kan hadin gwiwar da ake yi don neman zamanantar da Afirka, wadanda suka hada da tabbatar da adalci, da amfanawa juna, da kula da moriyar jama’a, da kare mabambantan al’adu, da inganta muhallin halittu, gami da samar da tsaro.

Idan an yi hadin gwiwa a duniya, bisa wadannan ka’idoji, to, za a iya tabbatar da babbar moriyar kasashen Afirka.

A zahiri, sai wata abokiyar gaske ce za ta iya gabatar da wannan shawara.

Na biyu kuma, sai a kwatanta matakan da mabambantan bangarori suka dauka.

Daniel Makokera, wani shahararren marubuci dan kasar Afirka ta Kudu, ya rubuta wani bayani a shafin yanar gizo na allAfrica a kwanan nan, inda ya kwatanta matakan kasar Sin da na kasar Amurka, dangane da Afirka.

A cewarsa, kasar Sin tana zuba jari don raya tattalin arzikin Afirka, inda take gina layin dogo, da na’urorin samar da wutar lantarki, da tashoshin jiragen ruwa, da yankunan masana’antu, da samar da ilimin sana’a, da fasahohin zamani, gami da daukar matakan soke harajin kwastam, da kare lafiyar jikin manoma ‘yan Afirka, da dai sauransu.

Yayin da kasar Amurka, a nata bangare, manufarta ta kan zama shiri da magana kawai, inda maganar ta kan sauya tsakanin gargadi game da “tarkon bashi”, da suka kan yadda ake gudanar da mulki a kasashen Afirka.

Lokacin da kasar Afirka ta Kudu ta karbi bakuncin taron kolin G20 na wannan karo, kana daukacin nahiyar Afirka ke alfahari da lamarin, kasar Amurka ta ce wai ana wa fararen fata “kisan kare dangi” a kasar Afirka ta Kudu, don haka ta ki tura manyan jami’anta su halarci taron.

A cewar mista Makokera, Amurka tana yin biris da nahiyar Afirka da gangan, don bata son ganin yaduwar ra’ayin cudanyar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da tasowar nahiyar Afirka.

Ko da yake kasar Sin tana kallon nahiyar Afirka a matsayin babbar abokiya mai muhimmanci, kasar Amurka na ci gaba da neman hana kasashen Afirka shiga cibiyar dandalin harkokin siyasa na duniya.

Mista Makokera ya kara da cewa, sakon kasar Sin ga kasashen Afirka shi ne, “ Za mu yi kokari tare don tabbatar da makoma mai haske, amma ba zan taba tilasta muku bin wata turbar raya tattalin arziki ba.” Wannan shi ne abin da ya kamata aboki mai gaskiya ya yi.

Abokantaka ta gaske dake tsakanin Afirka da Sin za ta haifar da wani sabon tsarin duniya, in ji Makokera.

A nan gaba, za mu kara fahimtar muhimmancin taron G20 na wannan karo, saboda ta ba da damar bambanta abokin gaske da wanda ba na gaske ba, da kuma nuna yanayin huldar dake tsakanin Afirka da Sin, da zai zama mai karin inganci a nan gaba. (Bello Wang)

 

G20
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
G20
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Next Post
Karin Kasashe Masu Tasowa Sun Shiga Aikin Sarrafa Harkokin Tattalin Arzikin Duniya

Karin Kasashe Masu Tasowa Sun Shiga Aikin Sarrafa Harkokin Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.