ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron G20: Afirka Tana Da Wata Abokiyar Gaske

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
G20

Wace ce abokiyar gaske ta nahiyar Afirka? Kasar Sin ce.

Taron kolin G20 da ya gudana a kasar Afrika ta Kudu a kwanan nan ya tabbatar da hakan.

To, ta yaya za a bambanta abokai na gaske, da wadanda ba su da gaskiya?

ADVERTISEMENT

Da farko, duba ko za su mai da hankali kan moriyarka.

A lokacin taron kolin G20 na wannan karo, kasar Sin da kasar Afirka ta Kudu sun gabatar da shawarar yin hadin gwiwa don zamanantar da nahiyar Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin

A cikin shawarar, an lura da bukatar kasashen Afirka ta zamanantarwa, kana an tsara wasu ka’idoji kan hadin gwiwar da ake yi don neman zamanantar da Afirka, wadanda suka hada da tabbatar da adalci, da amfanawa juna, da kula da moriyar jama’a, da kare mabambantan al’adu, da inganta muhallin halittu, gami da samar da tsaro.

Idan an yi hadin gwiwa a duniya, bisa wadannan ka’idoji, to, za a iya tabbatar da babbar moriyar kasashen Afirka.

A zahiri, sai wata abokiyar gaske ce za ta iya gabatar da wannan shawara.

Na biyu kuma, sai a kwatanta matakan da mabambantan bangarori suka dauka.

Daniel Makokera, wani shahararren marubuci dan kasar Afirka ta Kudu, ya rubuta wani bayani a shafin yanar gizo na allAfrica a kwanan nan, inda ya kwatanta matakan kasar Sin da na kasar Amurka, dangane da Afirka.

A cewarsa, kasar Sin tana zuba jari don raya tattalin arzikin Afirka, inda take gina layin dogo, da na’urorin samar da wutar lantarki, da tashoshin jiragen ruwa, da yankunan masana’antu, da samar da ilimin sana’a, da fasahohin zamani, gami da daukar matakan soke harajin kwastam, da kare lafiyar jikin manoma ‘yan Afirka, da dai sauransu.

Yayin da kasar Amurka, a nata bangare, manufarta ta kan zama shiri da magana kawai, inda maganar ta kan sauya tsakanin gargadi game da “tarkon bashi”, da suka kan yadda ake gudanar da mulki a kasashen Afirka.

Lokacin da kasar Afirka ta Kudu ta karbi bakuncin taron kolin G20 na wannan karo, kana daukacin nahiyar Afirka ke alfahari da lamarin, kasar Amurka ta ce wai ana wa fararen fata “kisan kare dangi” a kasar Afirka ta Kudu, don haka ta ki tura manyan jami’anta su halarci taron.

A cewar mista Makokera, Amurka tana yin biris da nahiyar Afirka da gangan, don bata son ganin yaduwar ra’ayin cudanyar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da tasowar nahiyar Afirka.

Ko da yake kasar Sin tana kallon nahiyar Afirka a matsayin babbar abokiya mai muhimmanci, kasar Amurka na ci gaba da neman hana kasashen Afirka shiga cibiyar dandalin harkokin siyasa na duniya.

Mista Makokera ya kara da cewa, sakon kasar Sin ga kasashen Afirka shi ne, “ Za mu yi kokari tare don tabbatar da makoma mai haske, amma ba zan taba tilasta muku bin wata turbar raya tattalin arziki ba.” Wannan shi ne abin da ya kamata aboki mai gaskiya ya yi.

Abokantaka ta gaske dake tsakanin Afirka da Sin za ta haifar da wani sabon tsarin duniya, in ji Makokera.

A nan gaba, za mu kara fahimtar muhimmancin taron G20 na wannan karo, saboda ta ba da damar bambanta abokin gaske da wanda ba na gaske ba, da kuma nuna yanayin huldar dake tsakanin Afirka da Sin, da zai zama mai karin inganci a nan gaba. (Bello Wang)

 

G20
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa
G20
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
  • Sulaiman
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

MASU ALAKA

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

July 1, 2026
Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin

June 30, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
Karin Kasashe Masu Tasowa Sun Shiga Aikin Sarrafa Harkokin Tattalin Arzikin Duniya

Karin Kasashe Masu Tasowa Sun Shiga Aikin Sarrafa Harkokin Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.