ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron G20: Afirka Tana Da Wata Abokiyar Gaske

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
G20

Wace ce abokiyar gaske ta nahiyar Afirka? Kasar Sin ce.

Taron kolin G20 da ya gudana a kasar Afrika ta Kudu a kwanan nan ya tabbatar da hakan.

To, ta yaya za a bambanta abokai na gaske, da wadanda ba su da gaskiya?

ADVERTISEMENT

Da farko, duba ko za su mai da hankali kan moriyarka.

A lokacin taron kolin G20 na wannan karo, kasar Sin da kasar Afirka ta Kudu sun gabatar da shawarar yin hadin gwiwa don zamanantar da nahiyar Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

A cikin shawarar, an lura da bukatar kasashen Afirka ta zamanantarwa, kana an tsara wasu ka’idoji kan hadin gwiwar da ake yi don neman zamanantar da Afirka, wadanda suka hada da tabbatar da adalci, da amfanawa juna, da kula da moriyar jama’a, da kare mabambantan al’adu, da inganta muhallin halittu, gami da samar da tsaro.

Idan an yi hadin gwiwa a duniya, bisa wadannan ka’idoji, to, za a iya tabbatar da babbar moriyar kasashen Afirka.

A zahiri, sai wata abokiyar gaske ce za ta iya gabatar da wannan shawara.

Na biyu kuma, sai a kwatanta matakan da mabambantan bangarori suka dauka.

Daniel Makokera, wani shahararren marubuci dan kasar Afirka ta Kudu, ya rubuta wani bayani a shafin yanar gizo na allAfrica a kwanan nan, inda ya kwatanta matakan kasar Sin da na kasar Amurka, dangane da Afirka.

A cewarsa, kasar Sin tana zuba jari don raya tattalin arzikin Afirka, inda take gina layin dogo, da na’urorin samar da wutar lantarki, da tashoshin jiragen ruwa, da yankunan masana’antu, da samar da ilimin sana’a, da fasahohin zamani, gami da daukar matakan soke harajin kwastam, da kare lafiyar jikin manoma ‘yan Afirka, da dai sauransu.

Yayin da kasar Amurka, a nata bangare, manufarta ta kan zama shiri da magana kawai, inda maganar ta kan sauya tsakanin gargadi game da “tarkon bashi”, da suka kan yadda ake gudanar da mulki a kasashen Afirka.

Lokacin da kasar Afirka ta Kudu ta karbi bakuncin taron kolin G20 na wannan karo, kana daukacin nahiyar Afirka ke alfahari da lamarin, kasar Amurka ta ce wai ana wa fararen fata “kisan kare dangi” a kasar Afirka ta Kudu, don haka ta ki tura manyan jami’anta su halarci taron.

A cewar mista Makokera, Amurka tana yin biris da nahiyar Afirka da gangan, don bata son ganin yaduwar ra’ayin cudanyar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da tasowar nahiyar Afirka.

Ko da yake kasar Sin tana kallon nahiyar Afirka a matsayin babbar abokiya mai muhimmanci, kasar Amurka na ci gaba da neman hana kasashen Afirka shiga cibiyar dandalin harkokin siyasa na duniya.

Mista Makokera ya kara da cewa, sakon kasar Sin ga kasashen Afirka shi ne, “ Za mu yi kokari tare don tabbatar da makoma mai haske, amma ba zan taba tilasta muku bin wata turbar raya tattalin arziki ba.” Wannan shi ne abin da ya kamata aboki mai gaskiya ya yi.

Abokantaka ta gaske dake tsakanin Afirka da Sin za ta haifar da wani sabon tsarin duniya, in ji Makokera.

A nan gaba, za mu kara fahimtar muhimmancin taron G20 na wannan karo, saboda ta ba da damar bambanta abokin gaske da wanda ba na gaske ba, da kuma nuna yanayin huldar dake tsakanin Afirka da Sin, da zai zama mai karin inganci a nan gaba. (Bello Wang)

 

G20
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin
G20
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • Sulaiman
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana
  • Sulaiman
    Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa
  • Sulaiman
    Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

MASU ALAKA

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi
Ra'ayi Riga

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

July 24, 2026
Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026
Next Post
Karin Kasashe Masu Tasowa Sun Shiga Aikin Sarrafa Harkokin Tattalin Arzikin Duniya

Karin Kasashe Masu Tasowa Sun Shiga Aikin Sarrafa Harkokin Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
G20

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.