ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Obi Ya Yi Alkawarin Biyan Kudin Jarrabawar NECO Na Fursunoni 148

by Idris Aliyu Daudawa
7 days ago
Obi

Tsohon dan takarar Shugaban kasa a karkashin jam’iyya Labour Party, Mista Peter Obi, ya yi alkawarin zai biya kudin jarabawar (NECO) na fursunoni 148 wadanda suke zaune a gidajen gyara halin ka a sassa daban daban na Jihar Anambra.

Obi ya bayyana hakan ne bayan da ya gana da wakilan su fursunoni daga Awka, Onitsha, Nnewi da kuma Aguata na Jihar Anambra.

  • Babu Ɗalibin Da Aka Sace A Makarantar St. Peter’s A Nasarawa – ‘Yansanda
  • 2027: Ganduje Ya Gargaɗi Mambobin APC Kan Fara Tallata Masu Neman Takarar Gwamna Da Wuri

Fursunoni wadanda suke rubuta jarabawa NECO, na iya shiga matsala saboda rashin biyan kudaden jarabawar.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda bayanin alkalumma suka nuna wadanda aka kai ma Obi, Awka na da 50, Onitsha 36, Nnewi 25 da kuma Aguata 37, gaba daya fursunoni 148 ke nan.

Kowane dalibi zai biya ₦aira 30,050 a matsayin kudin jarabawa da kuma karin ₦aira 2,000 saboda wani abu daban, hakan yasa kudaden suka kasance Naira 32,050, gaba daya sun kai jimillar ₦aira milyan 4,741.400.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Haramta Karɓa Ko Sauyawa Ɗalibai Aji Kai Tsaye Zuwa SS3

Fadar Shugaban Kasa Ta Karrama Daliban Da Suka Nuna Hazaka A 2025

Tsohon gwamnan Jihar Anambra ya ba tawagar wakilan tabbacin cewar zai biya kudaden domin tabbatar da an barsu sun gama rubuta jarabawa ba tare da kawo masu wata matsala ba.

Ya ce zai yi aiki tare da masu ra’aytinsa da kuma magoya bayansa domin a samu dama ta tara kudaden da ake bukata.

“Zan rubuta ma wakilan ranar Litinin domin tabbatar da cewa za’a iya biyan kudin, wanda hakan zai sa fursunonin su ci gaba da rubuta jarabawa.

Tsohon gwamnan ya kara jaddada cewa ilimi ya kasance wani babban abu ne na gyara al’amura masu yawa, ya ce wuraren ko gidajen gyara halinka wasu wurare ne da ake gyara halayen masu laifi ba wai su kasance wuraren da za a rika azabtar da suu ba.Obi,wanda ba da dadewa bane ya kai ziyararar Jami’ar Jihar California, Sacramento, kan wadansu tsare tsare da suka hada da lamarin daya shafi bada shawara kan lamarin karatu da kuma wadanda suke tsare sanadiyar wani laifin da suka aikata, da kuma wasu daidaikun mutane.

Ya nuna rashin jin dadinsa akan yadda ba a bayar da dama ta samun ilimi ga wadanda suke gidan gyara halinka a sassa daban daban na kasa, inda yace ai rashin samun ingantaccen ilimin ne yake sa irin wadanda suke cikin halin aikata laifin da suka dama.

“Idan mutane suka kammala wa’adin gidajen gyara halinka, dole ne su kasance sun samu mallakar abubuwan da za su sa su taimakawa al’umma, da kuma sake sa kansu hanya madaidaiciya domin jin dadin rayuwarsu.

Shugaban Kasa Tinubu Ya Amince Da Kafa Shugabannin Hukumar Kula Da Jami’oi Karo Na 13

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya amince da nada Shugabannin Hukumar kula da Jami’oi ta kasa a karo na 13 (NUC), inda ya amince da Emeritus Farfesa Oluremi Raphael Aina, OFR ,a matsayin Shugaba .

Shugabannin Hukumar da ba’a dade da kaddamarwa ba, a ma’aikatar ilimi ta tarayya tare da Shugabannin hukumar binciken harkokin ilimi, da ci gaba (NERDC), Cibiyar harkokin Malamai ta kasa (NTI), da kuma hukumar ilimin bai daya (UBEC).

A na shi bayanin, Ministan ilimi, Dakta Tunji Maruf Alausa, ya bayyana cewa Shugaban kasa yayi matukar amincewa da su Shugabannin wajen bayar da shawarar data kamata saboda kwarewar da suke da ita,ilimin da suke da shi wajen yiwa Hukumar jagoranci yayin da shi bangaren ilimin yake aiki domin tabbatar da irin kudurin da gwamnatin tarayya take da shi a karkashin jagorancin Tinubu .

Ita ma hukumar kulawa da harkokin jami’oi ta yi maraba da sabbin Shugabannin nata inda ta yi fatan za su tafiyar da ayyukansu fiye da yadda kowa ya k e tsammani ta hanyar samar da nagarta, shigo da wasu abubuwa a fadin Jami; oin da suke illahirin kowane sako da lungu na Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Haramta Karɓa Ko Sauyawa Ɗalibai Aji Kai Tsaye Zuwa SS3
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ta Haramta Karɓa Ko Sauyawa Ɗalibai Aji Kai Tsaye Zuwa SS3

December 14, 2025
Fadar Shugaban Kasa Ta Karrama Daliban Da Suka Nuna Hazaka A 2025
Ilimi

Fadar Shugaban Kasa Ta Karrama Daliban Da Suka Nuna Hazaka A 2025

November 30, 2025
Majalisar Wakilai Ta Nemi A Ɗauki Sabbin Ma’aikata A Jami’o’in Nijeriya
Ilimi

Majalisar Wakilai Ta Nemi A Ɗauki Sabbin Ma’aikata A Jami’o’in Nijeriya

November 21, 2025
Next Post
Ranar Bikin Kasar Noma Ta Duniya: Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Bai Wa Kasar Noma Kariya

Ranar Bikin Kasar Noma Ta Duniya: Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Bai Wa Kasar Noma Kariya

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.