ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Bikin Kasar Noma Ta Duniya: Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Bai Wa Kasar Noma Kariya

by Abubakar Abba
9 months ago
Noma

Gwamnatin tarayya, ta nuna damuwarta kan yadda ake samun lalacewar kasar noma a fadin wannan kasa, inda ta bukaci a gagguta samar ingantattun sauye-sauye, domin bai wa kasar kariyar da ta kamata, musamman domin tabbatar da ganin an samu damar ci gaba da samar da wadataccen abinci a ƙasar.

Karamin Ministan Samar da Wadataccen Abinci, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi, ya yi wannan kira ne a Abuja wajen taron bikin ranar kasar noma ta wannan shekara da aka gudanar a Abuja, inda ya yi nuni da cewa; ta hanyar samar da ingantacciyar kasar noma, za a samu dorarren ci gaba da kuma samun wadataccen abinci.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Tara Naira Biliyan 160 A Noman Alkama
  • FAO Ta Horar Da Manoma 100 Kiwon Kifi A Kano

“Ingantacciyar kasar noma, na samar da amfanin gona da ya kai kashi 95 cikin 100, wanda kuma ‘yan kasar ke amfani da shi, sai dai ya bayyana cewa; kashi 33 cikin 100 na kasar noman, kusan duk ta zaizaye,” in ji Ministan.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, idan aka ce za a dawo da akalla kashi biyu zuwa uku na kasar noman, za a iya shafe nan da shekara 1000, ba a iya cimma hakan ba a wannan kasa.

Ministan ya kara da cewa, domin magance wannan matsala, ma’aikatar ta samar da wadataccen abinci tare da mayar da hankali kan bunkasa tsarin yin noma da suka hada da sauya yin noma zuwa wata gona da bai wa gandun dajin noma kulawar da ta kamata da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

“A watan da ya gabata, an kaddamar da shirin bai wa gonakin manoman kasar kulawar da ta kamata na kasa wato, NFSHS, wanda wasu manoma 600 da masu hadaka, suka samar da wajen da aka tsara na yin amfani da takin zamanin, domin kaucewa asarar da manoma ke yi da kuma yawan kashe kudade a wajen aikin noma.

“Shirin ya kuma hada da tanadar dakunan yin gwaje-gwajen kasar noma 774 da ke daukacin fadin kasar, wanda matasa da kuma mata ne za su tafiyar da su, tuni kuma an tanadi kayan aiki a jihohi 12 da ke kasar,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa, Nijeriya ta kasance daya daga cikin kasashen da suka kulla yarjejiyar ta Afirka ta samar da takin zamani a 2024, wadda aka rattaba hannu, a kasar NAIROBI, musamman domin samar da ingantaccen takin zamani tare da hadaka da abokan hadaka kamar su GIZ, AGRA, IITA, bankin duniya, shirin sasakawa na Afrika da sauransu.

Ya bayyana cewa, ana kuma kan ci gaba da gudanar da aikin gwajin kasar noma, a jihohi 12 na kasar nan, kuma an sanya wannan aiki a cikin kasafin kudi na bana.

Sabi ya bukaci a mayar da hankali, domin bai wa kasar noma kariyar da ta kamata, musamman domin kare ta daga lalacewa, wanda hakan zai iya shafar kokarin da ake yi a kasar na samar da wadataccen abinci.

A jawabinsa a wajen taron, mataimakin shugaban cibiyar nazarin kimiyyar kasar noma (NISS), Olumuyiwa James Jayeoba, ya sanar da cewa; zai yi wuya a samu amfanin gona da ake bukata, matukar kasar noma na da matsala.

Yawan samun karuwar al’umma, na kara haddasa samun zaizaiyar kasa da kuma samun gurbatar muhalli.

Ya sanar da cewa, cibiyar ta NISS na kara kokari, wajen bai wa kasar noma kulawar da ta kamata, inda ya kara da cewa; ana kuma ci gaba da samar da sauye-sauyen bai wa kasar noma, kariyar da ta kamata a karkashin aikin na NFSHS, wanda ake gudanar da shi ta hanyar sabuwar hadaka.

Ya yi kira ga masu kirkiro da dokoki da masu safiyin kasa da sauran ‘yan kasar nan, da su rungumi tsarin mutunta kasar noma, musamman domin bai wa kasar noma kulawar da ta kamata.

Noma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
NDLEA

NDLEA Ta Kama Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ga 'Yan Bindiga 'Gamboli' A Neja

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.