ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Bikin Kasar Noma Ta Duniya: Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Bai Wa Kasar Noma Kariya

by Abubakar Abba
6 months ago
Noma

Gwamnatin tarayya, ta nuna damuwarta kan yadda ake samun lalacewar kasar noma a fadin wannan kasa, inda ta bukaci a gagguta samar ingantattun sauye-sauye, domin bai wa kasar kariyar da ta kamata, musamman domin tabbatar da ganin an samu damar ci gaba da samar da wadataccen abinci a ƙasar.

Karamin Ministan Samar da Wadataccen Abinci, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi, ya yi wannan kira ne a Abuja wajen taron bikin ranar kasar noma ta wannan shekara da aka gudanar a Abuja, inda ya yi nuni da cewa; ta hanyar samar da ingantacciyar kasar noma, za a samu dorarren ci gaba da kuma samun wadataccen abinci.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Tara Naira Biliyan 160 A Noman Alkama
  • FAO Ta Horar Da Manoma 100 Kiwon Kifi A Kano

“Ingantacciyar kasar noma, na samar da amfanin gona da ya kai kashi 95 cikin 100, wanda kuma ‘yan kasar ke amfani da shi, sai dai ya bayyana cewa; kashi 33 cikin 100 na kasar noman, kusan duk ta zaizaye,” in ji Ministan.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, idan aka ce za a dawo da akalla kashi biyu zuwa uku na kasar noman, za a iya shafe nan da shekara 1000, ba a iya cimma hakan ba a wannan kasa.

Ministan ya kara da cewa, domin magance wannan matsala, ma’aikatar ta samar da wadataccen abinci tare da mayar da hankali kan bunkasa tsarin yin noma da suka hada da sauya yin noma zuwa wata gona da bai wa gandun dajin noma kulawar da ta kamata da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

“A watan da ya gabata, an kaddamar da shirin bai wa gonakin manoman kasar kulawar da ta kamata na kasa wato, NFSHS, wanda wasu manoma 600 da masu hadaka, suka samar da wajen da aka tsara na yin amfani da takin zamanin, domin kaucewa asarar da manoma ke yi da kuma yawan kashe kudade a wajen aikin noma.

“Shirin ya kuma hada da tanadar dakunan yin gwaje-gwajen kasar noma 774 da ke daukacin fadin kasar, wanda matasa da kuma mata ne za su tafiyar da su, tuni kuma an tanadi kayan aiki a jihohi 12 da ke kasar,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa, Nijeriya ta kasance daya daga cikin kasashen da suka kulla yarjejiyar ta Afirka ta samar da takin zamani a 2024, wadda aka rattaba hannu, a kasar NAIROBI, musamman domin samar da ingantaccen takin zamani tare da hadaka da abokan hadaka kamar su GIZ, AGRA, IITA, bankin duniya, shirin sasakawa na Afrika da sauransu.

Ya bayyana cewa, ana kuma kan ci gaba da gudanar da aikin gwajin kasar noma, a jihohi 12 na kasar nan, kuma an sanya wannan aiki a cikin kasafin kudi na bana.

Sabi ya bukaci a mayar da hankali, domin bai wa kasar noma kariyar da ta kamata, musamman domin kare ta daga lalacewa, wanda hakan zai iya shafar kokarin da ake yi a kasar na samar da wadataccen abinci.

A jawabinsa a wajen taron, mataimakin shugaban cibiyar nazarin kimiyyar kasar noma (NISS), Olumuyiwa James Jayeoba, ya sanar da cewa; zai yi wuya a samu amfanin gona da ake bukata, matukar kasar noma na da matsala.

Yawan samun karuwar al’umma, na kara haddasa samun zaizaiyar kasa da kuma samun gurbatar muhalli.

Ya sanar da cewa, cibiyar ta NISS na kara kokari, wajen bai wa kasar noma kulawar da ta kamata, inda ya kara da cewa; ana kuma ci gaba da samar da sauye-sauyen bai wa kasar noma, kariyar da ta kamata a karkashin aikin na NFSHS, wanda ake gudanar da shi ta hanyar sabuwar hadaka.

Ya yi kira ga masu kirkiro da dokoki da masu safiyin kasa da sauran ‘yan kasar nan, da su rungumi tsarin mutunta kasar noma, musamman domin bai wa kasar noma kulawar da ta kamata.

Noma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
NDLEA

NDLEA Ta Kama Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ga 'Yan Bindiga 'Gamboli' A Neja

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.