Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya gargaɗi ’yan jam’iyyar APC a jihar da su daina fara tallata ko bayyana wani a matsayin ɗan takarar gwamna na 2027.
Ya ce yanzu ba lokacin fara magana kan masu neman takara ba ne, kuma irin wannan abu na iya haifar da rabuwar kai a cikin jam’iyya.
- An Tsare Sojojin Nijeriya 11 A Burkina Faso Bayan Jirginsu Ya Yi Saukar Gaggawa
- ’Yan Bindiga Sun Sace Manomi, Sun Jikkata Ɗansa A Ƙauyen Kano
Gargaɗin ya biyo bayan wasu jagororin APC da suka ce Sanata Barau Jibrin ne zai yi takarar gwamna a 2027, lamarin da ya jawo cece-kuce.
Daga baya wani daga cikin magoya bayansa, Baffa Takai, ya janye goyon bayansa tare da bayar da haƙuri.
A hirarsa da BBC Hausa, Ganduje ya ce ya kamata ’yan jam’iyyar su daina kwatanta masu neman takara.
Ya ƙara da cewa a jira lokacinsa ya yi, sannan waɗanda suka cancanta su fito neman takarar.














