• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu

Sunan Mataimakin Shugaban Kasa Ya Yi Batan-dabo Cikin Kwamitin

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An nada mamba kuma jigo a jam’iyyar PDP sannan Sanatan da ke wakiltar mazabar Enugu ta Gabas, Chimaroke Nnamani a cikin kwamitin yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023 da ke karatowa.

Hakan na kunshe cikin jerin sunayen da aka fitar a daren ranar Juma’a inda aka nemi sunan mataimain shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo sama da kasa cikin jerin kwamitin yakin zaben na Tinubu aka rasa, inda aka rawaito cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya umarci mataimakin nasa da ya maida hankali kawai wajen gudanar da mulki.

  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Halarci Taron Ministocin BRICS
  • Dakarun Kasar Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Wanzar Da Zaman Lafiya

Kazalika, jam’iyyar ta ki sanya sunan tsohon kakakin majalisar dokokin tarayya, Yakubu Dogara, tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal; tsohon ministan ilimi, Chukwuemeka Nwajiuba da dan-gani-kashenin Tinubu, Adebayo Shittu, wadda ya jagoranci manyan kungiyoyin goyon bayan Tinunu, ‘Asiwaju Tinubu-Shettima Coalition for Good Governance’ dukka babu sunayensu.

A wata sanarwar da jami’in watsa labarai na kwamitin yakin neman zaben Tinubu/Shettima, Festus Keyamo (SAN) ya fitar, ya ce an cire sunan Osianbajo da sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha daga cikin kwamitin yakin zaben ne sakamakon umarnin da shugaba Buhari ya bayar na cewa su maida hankali wajen gudanar da harkokin mulkin Nijeriya a halin yanzu.

Jerin kwamitin yakin zaben mai mutum 422 da sakataren kwamitin yakin zaben, Hon. James Faleke ya fitar, kuma an gano cewa wasu jerin fitattun jigogin jam’iyyar babu sunayensu a ciki.

Labarai Masu Nasaba

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Kazalika, shugaba Muhammadu Buhari shine shugaban kwamitin yakin zaben, Bola Ahmed Tinubu kuma shine mataimakin shugaba na kwamitin yakin zaben APC, yayin da kuma gwamnan jihar Filato, Simon Bako Lalong ya kasance darakta-janar yakin neman zabe na Tinubu.

Tsohon shugaban jam’iyyar, Kwamared Adams Oshiomhole shine aka ayyana a matsayin mataimakin darakta-janar nay akin zaben a sashin ayyuka, sanna akwai sunayen gwamnoni, ministoci, ‘yan majalisu, jakadu, da wasu jiga-jigai cikin kwamitin yakin zaben na Tinubu.

A sanarwar ta Keyamo, ya ce sabanin yadda wasu rahotonni ke yawo na cewa an cire sunayen wasu na kusa-kusan Buhari cikin kwamitin yakin zaben da kokarin nuna cewa akwai Baraka a jam’iyyar, ya ce sam ba haka zancen yake ba, illa dai ya nuna cewa Buhari ne ya umarci Osinbajo da Boss da su maida hankali wajen gudanar da mulki.

“A matsayin jam’iyyar da ta san meye take yi da gwamnatin da ta san meye take yi, ba zai yiyu a kwashe dukkanun manyan jami’an gwamnati a ce su bar ayyukansu su shiga kwamitin yakin zabe ba. APC ita ce ke da ikon jan ragamar Nijeriya har zuwa ranar 29 ga watan Mayun 2023, don haka akwai bukatar wasu su fi maida hankali wajen gudanar da harkokin mulki ba zallar yakin zabe ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: OsinbajoTinubuYakin Neman ZabeZaben 2023
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsananin Zafin Kaye A Zaɓen Fidda Gwani Yasa Wike Sambatu – Babba Mazoji

Next Post

Wakilin Kasar Sin Ya Nuna Adawa Game Da Tsoma Baki Cikin Harkokin Gidan Burundi Ta Fakewa Da Kare Hakkin Dan Adam

Related

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

3 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

5 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

8 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

9 hours ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

9 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Wakilin Kasar Sin Ya Nuna Adawa Game Da Tsoma Baki Cikin Harkokin Gidan Burundi Ta Fakewa Da Kare Hakkin Dan Adam

Wakilin Kasar Sin Ya Nuna Adawa Game Da Tsoma Baki Cikin Harkokin Gidan Burundi Ta Fakewa Da Kare Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.