ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsananin Zafin Kaye A Zaɓen Fidda Gwani Yasa Wike Sambatu – Babba Mazoji

by Abdullahi Muh'd Sheka
4 years ago
Wike

Duk zantukan da ke futa daga bakin Mai girma Gwamnan Jihar Rivers Nelson Wike sambatu ne Kawai na Zafin Kaye da yasha a Zaɓen Fidda Gwani da aka gudanar a baya. Honarabul Zaharaddeen Babba Mazoji Tsohon Dan takarar kujerar Sanata a Shekara ta 2019 Kuma guda cikin Dattijan Jam’iyyar PDP a Jihar Katsina ne ya bayyana haka ga manema Labarai a Abuja.

Honarabul Zaharaddeen Babba Mazoji yace “na saurari tattaunawar da akayi dashi inda ya bayyana wasu maganganu da basu kamata ace sun fito daga bakin mutun irin Wike ba, Wanda mutum ne mai qima a wajena kasancewar ya bayar da gagarumar  gudunmawa a baya. Abin akwai mamaki Wanda tun kafin lokacin Zaɓen fidda Gwani lokacin wani taro da akayi a Legas mun bayar da shawara inda akayi watsi da bukatar nuna wani dan Takara daga wata shiyya wanda hakan baya cikin kudin tsarin mulkin Jam’iyyar PDP.

  • Da Gaske Atiku Ya Hakura Da Wike?

“Kuma Wike mantawa ya yi sune sukayi uwa kuma sukayi makarbiya wajen tabbatar da fitowar Shugaban Jam’iyyar PDP daga arewa domin a zatonsu shikenan sai Shugaban Kasa ya fito daga kudu? Sun manta wanca kudiri ko tattaunawa da akayi a Jihar Legas cewa Kujerar Shugaban Kasa ‘yace a ruwa ta mai rabo, an aminta duk Mai sha’awa ya fito ya tallata hajarsa. Kuma ai shi Wike dashi akayi takarar fidda  Gwani na Kujerar  Shugaban Kasa na Jam’iyyar PDP,  mai girma Alhaji Atiku Abubakar ya rangada shi da Kasa. Sannan ko a zantawar tasa ya tabbatar da cewa mulki Allah ke bada shi ga wanda yaso, shike nan Allah ya baiwa Atiku sai ciwon hassada ya bayyana? Inji Mazoji

ADVERTISEMENT

Da aka tambayeshi kan matsayar Wike da ‘yan barandarsa kan Ficewa daga tawagar yakin neman zaɓen Atiku, Mazoji ya bayyana cewa wannan Shure shure ne da baya hana mutuwa,  abinda Wike ya kamata ya fahimta Kashi 90%  na masu zugashi wasu mutane ne da ko a akwatinsu ba zasu iya katabus ba, wasu kuma tsoffin Gwamnoni ne data kare masu suke dan lasar abin sawa a baka daga Gwmna Wike, Wanda Ina tabbatarwa da Wike cewa sauran ‘yan Kwanaki wa’adin mulkinsa ya kare duk guduwa zasu yi su barshi. Yanzu haka wani adadi mai yawa daga cikin masu rajin goya masa baya (Wike) duk sun tabbatar da Atiku suke, Idan Kuma  sun koma kusa dashi su nuna suna tare dashi.

Da aka tambayeshi baya ganin cikin jawaban Wike ya nuna yana cikin Jam’iyyar ta PDP kuma zai ci gaba da yakarta? Babba Mazoji cewa ya yi, mu Wike ba wata barazana bace ga takarar Wazirin Adamawa, domin duniya ta fahimci Wike da ‘yan korensa Arewa ce basa kauna, kuma ya kamata na tunawa Wike idan mantawa ya yi, ya manta Shekara nawa Obasanjo ya yi akan karagar mulki, Shekara Nawa Goodluck ya yi Kuma Shekara nawa Dattijon arziki Alhaji Musa ‘Yar Adua ya yi akan mulki, duka kusan Shekara Goma Sha Huɗu’ ‘yan kudu suka yi suna mulkar mu, kuma sai yanzu da Allah ya kawo lokacin Atiku hassada zata bayyana?

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Babba Mazoji ya tabbatarwa da masu irin wancan ciwon hassada cewa suyi hakuri mulki Allah ke ba dashi ga wanda yaso, yanzu kuma alamu sun bayyana Wazirin Adamawa Alhaji Atiku Abubakar shi ne Shugaban kasarmu na gobe da yardar Allah. Jama’ar Nijeriya Mun sha azaba a hannun Jam’iyyar APC, ga talauci, rashin tsaro, Yajin aikin Malaman Jami’a, Sayar da kadarorin Gwamnati, Jama’a duk sun zama mahaukata saboda tsananin yunwa, wannan tasa Jama’ar  Nijeriya yanzu sun gamsu Jam’iyyar PDP itace Jirgin fiton Al’umma.

A Karshe Babba Mazoji ya yiwa Jama’ar Kasarnan busharar kyawawan manufofin Atiku Abubakar, wanda zarar Allah ya bashi wannan dama aiwatarwa kawai za’a fara, ba kamar Gwamnatin APC ba data hau mulki babu wasu kwararan munufofin ciyar da Kasa gaba. Muna sanar da Jama’a sauran kwanki kadan ya rage a kaddamar da yakin neman zabe, wanda kowa zaiga irin fitar da zamuyi domin gaisawa da al’ummar Kasa.

Wike
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu

An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.