• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Matasa A Kano Sun Yi Alkawarin Yi Wa ‘Yan Siyasa Masu Ingiza Su Shaye-shaye Tutsu -Fatima Jikan Dan’uwa

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Rahotonni
0
2023: Matasa A Kano Sun Yi Alkawarin Yi Wa ‘Yan Siyasa Masu Ingiza Su Shaye-shaye Tutsu -Fatima Jikan Dan’uwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

28 ga watan Satumbar da ya gabata ne Hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa ta ayyana sakin takunkumin fara yakin neman zaben Shekara ta 2023, wanda hakan ke nuni da cewa kakar zaben ta kankama.

Akan haka Gidauniyar da ke yaki da Shan Miyagun Kwayoyi ta Kasa YADAF Karkashin Jagorancin Shugabar Gidauniyar Hajiya Fatima Bature Jikan Dan-Uwa ta bayyana fito da wasu tsare tsaren domin dakile al’adar wasu ‘yan siyasa dake durawa matasa Kayan maye domin biyan bukatun kansu.

  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Tsoho Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Har Abada Kan Laifin Fyade A Jigawa
  • Kotun Daukaka Kara Ta Umurci Kungiyar ASUU Da Ta Gaggauta Janye Yajin Aikin Da Take

Hajiya Fatima Bature JikanDan-Uwa ta bayyana Haka ne a lokacin kaddamar zagayen matattaran masu sayarwa tare ta Shan Miyagun Kwayoyi a Kano, Shirin Wanda shi ne irin sa na farko da wata kungiya ke tattalin kafa da kafa har matattarar matasa inda ake tattaunawa da su Kan dalilan da Suka jefa su cikin wannan mummunar ta’ada.

Ya ce jama’a kowa zai yi mamakin Jin dalilan wasu yaran na hakura da harkar Karatu sun gwammace afkawa cikin wannan harka ta shaye shaye.

“Wani abin mamaki da yawayaran da Gidauniyar YADAF tazanta dasu alokacin data Fara wannan zagayen kwakwaf, sun bayyana cewa Matsalar Jarrabawar Kualify ce sanadiyyar fadawa harkar Shaye-Shaye, a cewar yaran yaro yaci credit 8 Amma Gwamnati ya ce ba zata biya Masa tallafin kudin Jarrabawar ba sai abin da ya Kama daga credit 9 zuwa sama, sannan ga halin matsin tattalin arziki da ake fama dashi a kasa baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Wannan ta sa iyaye basa iya kashe wadannan makudan kudade domin biya wa yaransu Jarrabawar.

Saboda haka dole zaman Gida ya kama su,Kuma akan Haka sai ake gamuwada wasu da suka Jima a cikin harkar suna ba su shawarar Shan abinda zai rage masu wannan radadi daga nan Suka tsinci kansu a irin wannan Hali.

Hajiya Fatima Bature Jikan Dan-Uwa ta ci gaba cewa zuwa yanzu da muke wannan zagayen matattaran matasa mun sama da matasa 70 da Suka Kawo kansu domin Mayar da su makarantunsu, wannan Gidauniya ta Mayar da su tare da biya masu kudaden Jarrabawar, yanzu Haka akwai sansanin guda da tuni ya tashimatasan duk mun Mayar da su Makarantu. Ya ce  wannan na nuni da cewa zaben Shekara 2023 a Kano Babu matasa masu shaye-shaye a cikinsa, kowa ya Koma makaranta sauran Kuma tuni mun kammala Shirin bude cibiyar koyar da sana’o’i domin matasa su samu sana’ar dogaro da Kai maimakon bin ‘yan siyasar da su’ya’yansu na tura suna Karatun,mu Kuma an bar yaranmu ana takashe su ba gaira ba dalili.

Domin tabbatar da hadin guiwa da Hukumomin tsaro, Muna tunawa Hukumar zaben dokar da Gwamnati ta samar na tabbatar da gwajin kwakwalwar duk wani Mai bukatar yin takara domin tabbatar ba ya mu’amala da Miyagun Kwayoyi, ta ce a wannan gaba dole a jinjinawa Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, wanda shi tun a zabukan baya ya fara gwada wannan doka inda aka tabbatar da Sai da aka tura duk wani dan takara a Kano Hukumar da ke yaki da sha tare da fataucin Miyagun Kwayoyi NDLEA, inda aka tantace ‘yan takarkarun, har ma aka dakatar da wasu da aka samu da Matsalar shaye-shaye a cikinsu.

Ya ce yanzu haka za mu yi amfani da matasa tare da duk mai kishin ci gaban Jihar Kano da kuma masu yi wa Kano da Kasa fatan alhairi, domin bibiyar duk wani dan takara da ya nuna rashin kulawa da wannan doka ta kaucewa raba wa matasa kwayan maye a lokacin yakin neman zabe, zamu kuma bayyanawa duniya abin da muka samu kan haka, sannan zamu hada hannuda Jami’an Hukumar NDLEA domin kwarmata duk wanda ya tanadi kayan maye domin gurbata hankulan matasa.

“Sashin mu na tattaunawa da masu irin wannan matsala sun bayyana mana yadda wasu ‘yan siyasa ke amfani da matasa ta hanyar basu kayan maye domin samun damar cin karensu babu babbaka, saboda haka tuni wasu daga cikin ire-iren wadannan matasa sun zubar da makamansu tare alkawarin yin aiki tare da wannan Gidauniya domin ganin ba a yi amfani da matasan ba Wajen badakala a lokacin yakin neman zabe da ma lokacin Zaben ba.

Hajiya Fatima ta bayyana nasarar da wannan Gidauniyata samu daga lokacin kafuwarta zuwa yau, ta ce mun samu nasarar ziyartar Sarakuna, manyan attajirai, Jami’an Gwamnati, Malamai da limamai domin ganinmun hada hannu wajen yakar wannan babbar matsàla.

Wanda zuwa yanzu muna kara yiwa Allah godiya domin kwalliya na biyan kudin sabulu. Daga nan sai Hajiya Fatima Bature Jikan Dan-Uwa tayi amfani da wannan dama Wajen jan hankalin iyaye wajen lura da mutanen da yaransu ke mu’amala da su, domin abokai na taka muhimmiyar rawa wajen lalata rayuwar matasan wannan lokaci.

Haka ita ma tsangwama, rabuwar iyali, talauci da Matsalar rayuwar zaman aure na cikin abubuwan da ke jefa wasu matasan cikin wannan mummunan ta’ada.

A karshe Hajiya Fatima Bature ta bukaci hadin kan iyaye, Malamai, Sarakuna, Gwamnatoci da dukkan masu ruwa da tsaki domin hada hannu wajen tunkarar wannan matsala.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan SiyasaGidauniyakanoKayan MayeMatasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Mika Dakin Adana Magunguna Na Zamani Ga Zimbabwe

Next Post

Mauludi: Buhari Ya Bukaci ’Yan Siyasa Su Guje Wa Amfani Da Kalaman Batanci

Related

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

11 hours ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

6 days ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

6 days ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

2 months ago
Next Post
Mauludi: Buhari Ya Bukaci ’Yan Siyasa Su Guje Wa Amfani Da Kalaman Batanci

Mauludi: Buhari Ya Bukaci ’Yan Siyasa Su Guje Wa Amfani Da Kalaman Batanci

LABARAI MASU NASABA

Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.