• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Makarantar ‘Family Support Programme’ Ta Shirya Taron Lakcoci Ga Ɗalibai Sama Da 100 A Katsina

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Labarai
0
Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Makarantar ‘Family Support Programme’  Ta Shirya Taron Lakcoci Ga Ɗalibai Sama Da 100 A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar tsofaffin ɗaliban makarantar Family Support Programme wato Family Support Programme Old Students Association (FASPOSA) ajin 2018 ta shirya taron lakcoci daban-daban ga ɗalibai sama da guda 100 ‘yan makarantar.

Taron ya gudana ne a babban ɗakin taron makarantar kuma ya samu halartar wasu daga cikin malamai, mambobi da shugabannin ƙungiyar, har ma da manyan baƙin da suka zo daga wajen makarantar.

  • Tukunyar Gas Ta Yi Bindiga, Ta Yi Ajalin Wata Mata A Kwara
  • “CBN Na Da Goyon Bayana Wajen Sauya Fasalin Naira” —Buhari

Taken taron mai suna ‘CHANGE THE WORLD’ wato ‘A CANZA DUNIYA’ ya samo asali ne bisa irin yadda matasa masu tasowa suke da muhimmiyar rawa wurin canza duniya.

Tsofaffin
Wasu daga cikin shugabannin kungiyar tsofaffin daliban makarantar mata

Batutuwan da aka yi lakca akan su sun haɗa da; muhimmancin sana’a a ƙarni na ashirin da ɗaya, illar shaye-shaye da kuma rashin maida hankalin ɗalibai a makarantun Sakandare.

Daga bisani kuma, an gabatar da wasannin kwaikwayo tare da rubutattun waƙoƙin harshen Turanci masu nishaɗantarwa, wa’azantarwa, ilimantarwa da ƙayatarwa.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

GORON JUMA’A 09/05/2025

Tsofaffin
Wasu daga cikin shugabannin kungiyar tsofaffin daliban makarantar mata

Da yake jawabi a lokacin taron, shugaban ƙungiyar Auwal Ibrahim, ya bayyana cewa an shirya wannan taron wayar da kai ga daliban domin ilimantar da su akan illar shan miyagun ƙwayoyi, illar satar jarabawa da yadda za su koyi sana’o’i domin dogaro da kansu.

Ya yi kira ga dukkan daliban da su ƙaurace tare da nisantar dukkanin wani nau’in kayan maye saboda hakan ka iya sa rayuwarsu cikin halin ƙaƙani’kayi da lalacewar rayuwa, saboda hakan domin ganin sun inganta rayuwa to tabbas su tabbatar sun guji tare da nisantar kayan maye.

Domin ta’ammali da miyagun ƙwayoyi babu abin da yake jaza wa sai lalata rayuwa.

Tsofaffin
Wasu daga cikin shugabannin kungiyar tsofaffin daliban makarantar

Mataimakiyar shugaban kungiyar, Maryam Aminu Saulawa a jawabin da ta yi kira ga dalibai musamman mata akan muhimmancin ilimin ƴaƴa mata, inda ta jawo hankalinsu da su maida hankali akan karatunsu domin ganin sun cimma gaci a rayuwarsu ta nan gaba.

Ta yi kira ga ƴaƴa mata da su kuma tashi su nemi sana’a musamman ƙananan sana’o’i irin wanda mata ke iyayi a cikin gida ba tare da sun bar gidajen iyayansu ba, domin hakan zai taimaka wa rayuwar wajen ganin cewa sun dogara da kansu.

Wakilin shugabar makarantar malam Abubakar Sa’idu, ta nuna jin daɗinta bisa yadda daliban suka cimma nasara a rayuwarsu, da ya sanya suka waiwayo ƙannensu domin bada gudunmawarsu ga ci gaban makarantar.

Tsofaffin
Dalibai na sauraren lakca

Abubakar Sa’idu, ya ce makarantar tana alfahari da su kan wannan kyakkyawan aiki da suke yi, sai ya buƙace su da su ɗore da hakan domin cibgaban ilimi a makarantar da Jihar Katsina da ma ƙasa baki ɗaya, da kuma samar da al’umma tsaftatacciya.

A jawabinsu daban-daban uwar ƙungiyar Misis Fatima Abdullahi da Misis Hajara Korau da kuma malam Musa Umar sun jinjina wa tsofaffin daliban a bisa shirya wannan taro, inda suka bayyana cewa abubuwan da suka tattauna ya yi dai-dai da matsalolin da ake fuskanta a Jihar Katsina, wanda ake buƙatar gudunmuwar kowa a kan haka.

A jawabin skataren ƙungiyar, Sulaiman Nasir shi ma yayi kira ga daliban maza da mata da su maida hankali a karatunsu kuma su ƙauracewa duk wata hanya da ka iya jaza musu satar amsa a lokacin jarabawa, saboda hakan babbar illa ce ga ɗalibi mai neman ilimi.

Tsofaffin
Wasu daga cikin daliban da aka shirya wa lakca

Sakataren ƙungiyar ya kuma kara da cewa su tashi su nemi sana’a musamman maza, inda ya ce za su iya fara koyon aikin hannu misali: kafinta, kanikanci, fenti, gyaran wutar lantarki da dai sauransu, tun daga yanzu, wato tun suna da ƙuruciyarsu domin hakan zai taimaka musu, da kuma inganta rayuwarsu a shekaru masu zuwa.

Abdulrahman Ibrahim Hassan, jami’in hulda da jama’a na ƙungiyar, ya ce wannan shi ne karon farko da wannan ƙungiya ta shirya irin wannan taro domin ci gaban ɗalibai, ya kuma kara da cewa “In sha Allahu za mu ci gaba da aiwatar da dukkan kyawawan abubuwa ire-iren waɗannan domin ci gaban ɗalibai da matasa har ma da sauran al’umma.”

Daga ƙarshe, malamai da hukumar makarantar sun nuna jin daɗinsu akan irin wannan ci gaba da tsofaffin ɗalibanta suka kawo, sun kuma yi godiya tare da jaddada goyon bayansu akan dukkan abubuwa irin waɗannan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci Gaban MatasaKatsinaKungiyar Tsofaffin DalibaiLakcociMakaranta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tukunyar Gas Ta Yi Bindiga, Ta Yi Ajalin Wata Mata A Kwara

Next Post

Mutuwar Dan Davido: PDP Ta Dakatar Da Tarukan Siyasa A Jihar Osun

Related

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

51 minutes ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

2 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

3 hours ago
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

4 hours ago
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote
Labarai

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

5 hours ago
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

6 hours ago
Next Post
Mutuwar Dan Davido: PDP Ta Dakatar Da Tarukan Siyasa A Jihar Osun

Mutuwar Dan Davido: PDP Ta Dakatar Da Tarukan Siyasa A Jihar Osun

LABARAI MASU NASABA

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.