• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoma Sun Koka Kan Hauhawar Farashin Takin Zamani

by Sulaiman and Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoma Sun Koka Kan Hauhawar Farashin Takin Zamani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Takin zamani na gwamnatin tarayya mai lamba 20:10:10, ta kayyade farashinsa a kan naira 5,500, amma a yanzu, farashinsa ya kai sama da naira 14,000 wanda kuma ba dukkan manoma ke iya saye ba.

A kalla a cikin wata shida da suma wuce, farashin takin zamani na ci gaba da tashin gwaron Zabi, inda hakan ya janyo manoma a fadin kasar nan, ke ci gaba da koka wa.

  • Rahoton Karya Da Adrian Zenz Ya Watsa Ya Tona Asirin Amurka

A watan Janairun 2022 an sayar da buhun takin daya, daga naira 11,000 zuwa naira 16,000 amma a yanzu, ana sayar da buhu daya daga naira 24,000 zuwa naira 30,000, amma ya danganta da irin nau’insa ko kuma gurin da ake sayar da shi.

Ko da yake, matsalar ba Nijeriya kadai ta shafa ba, abu ne da ya shafi kusan duniya baki daya amma a Nijeriya matsalar har ta kai wasu daga cikin manoma bango.

A yankun da dama a Nijeriya manoma ba sa iya yin noma ba tare da yin amfani da takin ba, musamman a inda ba a samun kasar noma mai inganci.
Ci gaba tashin farashin ya tilasta manoma da dama wajen yin amfani da takin gargajiya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

Ratotanni daga sassan Nijeriya sun nuna cewa, farashinsa na ci gaba da tashi, inda ake ganin zai ci gaba da tashi a watanni masu zuwa.
A garin Abuja da kewaye da jihohin Neja da Nasarawa.

Nau’in Indorama da Dangote da Notore su ne ake sayar wa daga naira 19,000 zuwa naira 25,000.
NPK, musamman 15:15:15 farashin buhu daya mai nauyin kilogiram 50, ya kai naira 30,000, wannan ya danganta da irin nau’insa.

Binciken da aka gudanar a jihar Kano, ya nuna cewa, farashin nau’insa samfarin Indorama a yanzu ya kai naira 22,000, sabanin farashin naira 12,000 da aka sayar a 2021,inda samfarin Dangote a yanzu, ya kai naira N19,000 sabanin naira 9,000 a 2021, haka kuma farashin samfarin Waraka, a yanzu ana sayar da shi a kan naira 25,000 sabanin naira 16,000 a 2021. Bugu da kari, samfarinsa na NPK 15:15:15 wato na Nagari a yanzu ana sayar da shi a kan naira 24,500 sabanin N12,000, NPK 20:10;10 a 2021, inda samfarin Golden Penny a yanzu ana sayar da shi a kan naira 25,000 sabanin naira 13,000 NPK 20:10:10 na Kasco a yanzu ana sayar da shi a kan naira N15,000 sabanin naira 9,500.

Malam Danladi Balarabe, manomi a karamar hukumar Bagwai a ya ce, tsadar Takin zamani ya sa manoma da dama a yankin rugumar yin amfani da takin gargajiya kuma noman bana, ba dukkan manomi zai iya sayen Takin zamanin ba.
Shi ma wani manomi a karamar hukumar Kiru Muhammad Tahir ya ce, wasu manoma a yankin na tunanin fara yin amfani da wani sabon sanadarin Ruwa na takin zamani da wani kamfani ya gabatar wa manoma a yankin a matsayin takin zamani wanda kuma yana da saukin farashin.

A jihar Neja, manoma da dama sun koma yin amfani da bola a matsayin taki, inda wani manomi Mohammad Umar ya ce, tuni ya koma yin amfani Bola wajen noma Masara da Shinkafa saboda tsadar farashin takin zamani.

Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gano manoma na ainahi domin ta taimaka masu, musamman da takin zamani da kuma samar masu da kayan aikin noma a farashi mai sauki.
Adamu Aliyu, wani manomi a karamar hukumar Kacha a jihar ya sanar da cewa, yana yin amfani da kashin kaji ne a gonarsa domin farashin takin zamani a jihar ya yi tsada, inda ya kara da cewa, a baya yana sayen buhu daya na kashin kajin mai nauyin kilogirkm 100 kan naira 2,500 wanda shi ma farashin sa, ya kara tashi sama.

Shi ma wani manomi a karamar hukumar Gbako Muhammad Muhammad ya bayyana cewa, yin amfani da bola wajen yin noman ya fi masa sauki kan yin amfani da takin zamani, musamman saboda tsadarsa, inda ya kara da cewa, idan kana da naira 10,000 zaka iya yin hayar mota kirar pickup ta kwaso maka bola ta kai maka Gona maimakon sayen buhun takin zamani kan daga naira 22,000 ko kuma a kan naira 25,000.

Wani mai kiwon Kajin gisan Gona Suleiman Mohammed, ya tabbatar da cewa, suna sayar da buhu daya na takin kashin kaji mai nauyin kilogiram 100 a kan farashin naira 3,000.

Suleiman Mohammed ya kara da cewa, bukatarsa na kara yawa matuka, musamman ganin ana kara samun manoma da ke bukata a tanadar masu da kashin domin ba za ka kawai zo, kace kana bukata ka kuma samu a nan take ba manoman na biyan kudaden su ne da wuri, don a tara masu Kashin Kajin.
A cewar Suleiman Mohammed, wasu mutane sun rungumi sana’ar sayen Kashin Kajin domin su sayar wa da manoma.

“Bukatarsa na kara karuwa matuka, musamman ganin ana kara samun manoma da ke bukata a tanadar masu da kashin domin ba za ka kawai zo, ka ce kana bukata ka kuma samu a nan take ba manoman na biyan kudaden su ne da wuri, don a tara masu Kashin Kajin”.
A jihar Filato wasu manoma kamar su, John Ajiji na ci gaba da kokawa kan tashin farashin na Takin zamani a jihar inda suka bayyana cewa, tsadar farashin na Takin zamani, ya yi matukar janyo masu koma baya wajen gudanar da aikin noma, inda kuma hakan ya sa suke fuskantar wahala da ban da ban a fannin.
Ajiji wanda manomi ne a Jos ta Arewa Maso Gabas ya sanar da cewa, tsadar farashin na takin zamani ya sa ya rage yawan noman da yake yi domin bai da karfin da zai iya sayen takin zamani a kakar noamn bana.

Ya ci gaba da cewa, a baya a kowacce damina, ya na sayen Takin zamani Buhu 10 domin yin noma, amma a yanzu, ko buhu biyar ba zai iya saye ba.
Ajiji ya kara da cewa, a yanzu suna sayen takin zamani samfarin NPK Buhu daya a kan naira 28,000, inda kuma suke sayen buhu daya samfarin Urea a kan naira 21,000.

“A baya ako wacce damina, ya na sayen takin zamani buhu 10 domin yin noma, amma a yanzu, ko buhu biyar ba zai iya saye ba”.

A cewar John Ajiji, idan har ya na bukatar ya sayi Takin zamani mai yawa don yin amfani da shi a Ginarsa a yanzu sai in ya kashe sama da naira 100,000 zai iya saye.
“Idan har ya na bukatar ya sayi Takin zamani mai yawa don yin amfani da shi a Ginarsa a yanzu sai in ya kashe sama da naira 100,000 zai iya saye”.
John Ajiji ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta samar da wadataccen Takin zamani ga manoman da ke kasar nan musamman kananan manoma.

” Muna kira ga gwamnatin tarayya da ta samar da wadataccen takin zamani ga manoman da ke kasar nan musamman kananan manoma, musamman idan aka yi la’akari da kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi na wadata kasar nan da abinci mai ya wanda zai kuma kai ga ana fitar da shi zuwa sauran kasuwannin duniya domin sayar wa”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Daliban Shirin ‘N-Build’ Kashi Na ‘C1’ Sun Samu Horo Tare da Kayan Aiki

Next Post

Akeredolu Ya Soke Bikin Ranar DimokraÉ—iyya Ta Bana A Jihar Ondo

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

6 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

6 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

6 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
Akeredolu Ya Soke Bikin Ranar DimokraÉ—iyya Ta Bana A Jihar Ondo

Akeredolu Ya Soke Bikin Ranar DimokraÉ—iyya Ta Bana A Jihar Ondo

LABARAI MASU NASABA

aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.