ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

by Abubakar Sulaiman
11 months ago
NNPP

Ɗaya daga cikin jiga-jigan jam’iyyar NNPP, Alhaji Aminu Ringim, ya bayyana cewa tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, shi ne kaɗai ɗan siyasar da ya cancanta ya maye gurbin marigayi tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.

A wata hira da manema labarai a Abuja, Ringim ya ce irin ayyukan ci gaban ɗan Adam da na gine-gine da Kwankwaso ya yi a lokacin gwamnatinsa a Kano ne suka tabbatar da cancantarsa. Ya kwatanta Kwankwaso da fitattun shugabannin arewa kamar Sir Ahmadu Bello da Malam Aminu Kano, yana mai cewa ya tsaya tsayin daka wajen kare ‘yan ƙasa marasa ƙarfi.

  • Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
  • EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

Ringim ya bayyana Kwankwaso a matsayin ɗan siyasa na ƙasa baki ɗaya wanda ke da goyon baya a jihohin da suka haɗa da Katsina, Jigawa, Zamfara, Sokoto, da Kebbi, yana mai cewa irin tasirin da ya ke da shi ya zarce na jihohi ko yankuna. Ya ce: “Kwankwaso ya kafa tafiya mai zurfi fiye da jam’iyya. Ya gina gagarumin gungu na magoya baya, kuma har yanzu yana jan hankalin al’umma daga dukkanin sassa.”

ADVERTISEMENT

Ya jaddada cewa Kwankwaso ba wai kawai yana magana kan sauyi ba ne, ya kuma aiwatar da shi lokacin da ya kasance gwamna da kuma Ministan Tsaro. Daga cikin manyan ayyukansa akwai ilimi kyauta, da tallafin karatu na waje, da horon sana’o’in dogaro da kai. Ringim ya ce waɗannan su ne irin manufofin da suka ƙunshi falsafar Aminu Kano da kuma hangen nesa irin na Sardauna.

Dangane da yiwuwar komawar Kwankwaso APC, Ringim ya tabbatar da cewa akwai tattaunawa da ake yi ta bayan fage domin jawo shi cikin jam’iyyar. Ya ce: “Kwankwaso wani babban kayan siyasa ne da ba za a iya kyale shi ba. Ko da a APC, akwai masu son dawowarsa saboda yana da manufa mai amfani da al’umma.”

LABARAI MASU NASABA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

A cewar Ringim, idan ana so a sami cigaban da ya shafi kowa da kowa a Arewacin Nijeriya da ma ƙasa baki ɗaya, to ana buƙatar siyasa irin ta Kwankwaso wadda ke mayar da hankali kan talakawa da gaskiya a mulki.

NNPP
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina
  • Abubakar Sulaiman
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya

MASU ALAKA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

June 19, 2026
INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6
Manyan Labarai

INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6

June 19, 2026
Next Post
Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa

Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.