• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Daga Karshe Dai Tawagar Su Dogara Sun Mara Wa Atiku Baya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
2023: Daga Karshe Dai Tawagar Su Dogara Sun Mara Wa Atiku Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar jagororin kiristoci da musulmai ‘yan siyasa da suka fito daga jihohin arewa 19 da babban birnin tarayya Abuja sun ayyana goyon bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023 da ke tafe, Alhaji Atiku Abubakar a matsayin dan takarar da suka cimma matsayar mara wa baya.

Kungiyar wacce ta misalta goyon bayan tikitin takarar Atiku/Okowa a matsayin zabin da ya dace ga dukkanin masu neman adalci ga kowani bangare a kasar nan.

  • Dogara, Babachir Sun Gana Da Shugabannin Kiristoci Don Daukar Matsaya Kan Zaben 2023
  • Rayuwata Na Cikin Hatsari, Ana Kokarin Kashe Ni – Yakubu Dogara

Wannan matsayar na kunshe ne ta cikin wata sanarwar bayan taro da kungiyar jagororin suka yi a Abuja a ranar Juma’a dauke da sanya hannun tsohon shugaban marasa rinjaye na majalisar wakilai Hon. Mohammed Umara Kumalia da Barista Nunge Mele, (SAN) tare da raba kwafinta ga ‘yan jarida a Bauchi.

Idan za ku iya tunawa dai, gungun kiristocin wadanda suke karkashin tawagar su tsohon Kakakin majalisar tarayya, Yakubu Dogara wadanda suka kasance mambobin jam’iyyar APC ne a baya, sun yi ta gwagwarmayar yaki da tikitin Musulmi da Musulmi wanda suka sha alwashin ba za su mara wa dan takarar jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu baya ba.

Sanarwar kungiyar ya nemi dukkanin al’ummar Nijeriya da su mara wa PDP baya domin bai wa kowani bangare dama a cikin mulki a maimakon nuna wariya ga kiristoci ta hanyar yin tikiri musulmai biyu da APC ta yi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Sun yi tilawar cewa, kungiyar jagororin kiristoci da musulmai a arewa ta kafa wani kwamiti a ranar 8 ga watan Oktoba domin ya yi nazarin dan takarar da ya dace a mara wa baya cikin manyan ‘yan takarar shugaban kasa a zaben 2023 da ke tafe.

Kungiyar ta ce, a bisa nazarinta da bincikenta, tikitin takarar Atiku Abubakar na PDP ne kawai ya fi zama a’ala ga dukkanin al’ummar Nijeriya, kuma shine wanda ya fi dacewa a duk cikin manyan ‘yan takarar shugaban kasa guda hudu da suke nema a halin yanzu.

Daga bisani kungiyar sun sha alwashin cewa za su kasa su tsare har sai sun tabbatar APC ba ta samu nasara a zaben 2023 ba, domin a cewarsu an kitsa rashin adalci ga al’ummar kiristoci a yadda aka fitar da tsarin tikitin jam’iyyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023Dogara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Alfanun Noman Gyada Wajen Habaka Tattalin Arzikin Kasa 

Next Post

Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

1 hour ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

2 hours ago
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

2 hours ago
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
Labarai

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

4 hours ago
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
Labarai

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

4 hours ago
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule
Labarai

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

5 hours ago
Next Post
Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.