• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: PDP Ta Koka Bisa Matsin Lamba Da Ake Wa Mambobinta A Zamfara

by Hussein Yero
3 years ago
in Siyasa
0
2023: PDP Ta Koka Bisa Matsin Lamba Da Ake Wa Mambobinta A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP a Jihar Zamfara, ta koka kan zargin muzgunawar da jami’an tsaro da Gwamnatin Jihar Zamfara ke wa ‘ya’yanta na daure su a gidajen yari bisa yarfen siyasa.

Shugaban riko na jam’iyyar a jihar Hon. Mukhtar Lugga, ne ya bayyana haka a taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Gusau.

  • Abubuwan Lura Guda 6 Game Da Sabbin Dokokin CBN Na Mu’amalar Kudi
  • PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Lugga, ya zargi gwamnatin Jihar Zamfara tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro da kame mambobinsu bisa zarge-zarge marasa tushe bare makama kawai bisa abin da ya misalta kokarin firgitarwa da razanar da mamboninsu

Ya kuma bayyana cewa dan takarar Sanatan Zamfara ta Tsakiya na jam’iyyar kuma tsohon ministan yada labarai, Alhaji Ikra Aliyu Bilbis, ya shafe tsawon mako guda a tsare a gidan yari tare da gurfanar da shi gaban kotu kan zargin daukar nauyin ‘yan bangar siyasa wajen lalata allunan tallan jam’iyyar APC a babban birnin jihar.

“Kuma tsauraran sharuddan da kotu ta sanya na belinsa sun saba wa tsarin mulki da rashin adalci na sai ya kawo manyan sakatare wanda ke bakin aiki a yanzu ne kafin a bayar da belin .inistan, wanda ya saba wa hankali da doka wanda ba shi da gwamnati ta yaya zai kawo ma’aikacin gwamnati ya yi belinsa? Shugaban ya tambaya.

Labarai Masu Nasaba

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

Lugga ya kuma koka da yadda aka kama tare da daure tsohon jakadan Kasar Guinea Conarcri, Mai Riga Muhammad a matsayin wanda bai yi laifin komai ba sai don yana jam’iyyar PDP.

“Tsohon jakadan ya kwashe sama da wata guda a gidan yari kuma shari’arsa tana tafiyar hawauniya, kuma har yanzu ana yi mana barazana daga gwamnatin APC karkashin jagorancin Gwamna Bello Muhammad Matawalle tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro na kama duk wanda ya fito fili ya ayyana shi dan jam’iyyar PDP ne a Zamfara.”

Shugaban ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da jami’an tsaro na jihar da kuma babban Sufeton ‘yansanda a kan a taimake su kan halin da jam’iyyar PDP da mutanenta ke ciki na matsi da takurawa.

Ya kuma yi kira ga kasashen duniya da gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da su sa baki a cikin lamarin domin samun zaman lafiya don a halin yanzu dimokradiyya na fuskantar barazana a Jihar Zamfara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCPDPZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Nasarar Harba Tauraron Dan Adam Na Tattara Bayanan Kasa

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Kone Gidaje 22 A Gombe 

Related

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

3 hours ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

1 day ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

4 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

5 days ago
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

1 week ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

1 week ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Mutane A Masallaci A Delta

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Kone Gidaje 22 A Gombe 

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.