• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fitiyanul Islam Za Ta Kaddamar Da Asusun Taimaka Wa Marayu Ranar Alhamis Mai Zuwa

by Sulaiman
3 years ago
in Rahotonni
0
Fitiyanul Islam Za Ta Kaddamar Da Asusun Taimaka Wa Marayu Ranar Alhamis Mai Zuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar addinin Musulunci ta Fitiyanul Islam ta Nijeriya ta bayyana cewa za ta samar wa dubban marayun da hare-haren ta’addanci su ka raba su da iyayen su a faɗin ƙasar nan matsuguni.

Ƙungiyar ta ce saboda haka ne ma za ta ƙaddamar da wani asusu na musamman a ranar Alhamis mai zuwa, 15 ga Disamba, 2022 domin gina Gidan Marayu na Sheikh Ibrahim Inyass da Cibiyar Koyar da Sana’o’i a Zariya cikin Jihar Kaduna.

  • Rundunar Soji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6 A Borno

A sanarwar da ya rattaba wa hannu, Mataimakin Sakatare Janar na ƙungiyar, wanda kuma shi ne Shugaban babban kwamitin shirya taron na ƙasa, Dakta Musa Muhammad Imam, ya ce za a yi ƙaddamarwar ne a lokacin babban taron ƙungiyar na shekara-shekara wanda za a gudanar a ɗakin taro na Hukumar Jami’o’i ta Ƙasa (NUC) da ke Maitama, Abuja.

Ya ce haka kuma za a gudanar da zaɓen shugabannin ƙungiyar na ƙasa a washegarin ranar taron.

Dakta Imam ya ce babban baƙo na musamman shi ne Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, yayin da shugaban taron shi ne mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Sanata Kashim Shettima.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Fitiyanul Islam

Mataimakin babban sakataren ya ce babban mai ƙaddamarwa shi ne ɗan takarar shugaban ƙasa na APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, sannan babban baƙo mai jawabi shi ne Babban Limamin Masallacin Ƙasa da ke Abuja, Farfesa Ibrahim Maqari.

Ya ƙara da cewa uban taron shi ne Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, yayin da iyayen taro su ne Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi da Sheikh Shariff Ibrahim Saleh.

Sanarwar ta ce babban mai masaukin baƙi shi ne Ministan Gundumar Birnin Tarayya, Alhaji Muhammad Musa Bello, yayin da Sanata Abu Ibrahim da ɗan takarar gwamna na APC a Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, za su kasance masu taimaka masa.

Dakta Imam ya yi fatan ɗaukacin Musulmi za su yi ƙoƙari su halarci taron domin fa’idar sa.

Ita da ƙungiyar Fityanul Islam ta Nijeriya (FIN), an kafa ta ne a cikin 1962 a Kano a ƙarƙashin jagorancin Sheikh Ibrahim Inyass Al-Kaulahi (rta), kuma tun daga lokacin ta kasance mai taka muhimmiyar rawa wajen da’awar addinin Musulunci ta hanyar ɗaruruwan makarantun ta da ke cikin Nijeriya da sauran ƙasashen yankin Afrika ta Yamma.

Haka kuma ta kan yi aikin yaɗa koyarwar Annabi Muhammadu (s.a.w.), wanda ya haɗa da zaman lafiya da juna, da tsare dokokin addini da kuma neman ilimin addinin Islama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wasu Sojojin Chadi Sun Shiga Hannu Kan Yunkurin Kitsa Juyin Mulki A Kasar

Next Post

Qatar 2022: Buhari Ya Jinjina Wa Morocco Kan Daukaka Darajar Afirka

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
Fitiyanul Islam
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 month ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 month ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Qatar 2022: Buhari Ya Jinjina Wa Morocco Kan Daukaka Darajar Afirka

Qatar 2022: Buhari Ya Jinjina Wa Morocco Kan Daukaka Darajar Afirka

LABARAI MASU NASABA

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.