ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fitiyanul Islam Za Ta Kaddamar Da Asusun Taimaka Wa Marayu Ranar Alhamis Mai Zuwa

by Sulaiman
4 years ago
Fitiyanul Islam

Ƙungiyar addinin Musulunci ta Fitiyanul Islam ta Nijeriya ta bayyana cewa za ta samar wa dubban marayun da hare-haren ta’addanci su ka raba su da iyayen su a faɗin ƙasar nan matsuguni.

Ƙungiyar ta ce saboda haka ne ma za ta ƙaddamar da wani asusu na musamman a ranar Alhamis mai zuwa, 15 ga Disamba, 2022 domin gina Gidan Marayu na Sheikh Ibrahim Inyass da Cibiyar Koyar da Sana’o’i a Zariya cikin Jihar Kaduna.

  • Rundunar Soji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6 A Borno

A sanarwar da ya rattaba wa hannu, Mataimakin Sakatare Janar na ƙungiyar, wanda kuma shi ne Shugaban babban kwamitin shirya taron na ƙasa, Dakta Musa Muhammad Imam, ya ce za a yi ƙaddamarwar ne a lokacin babban taron ƙungiyar na shekara-shekara wanda za a gudanar a ɗakin taro na Hukumar Jami’o’i ta Ƙasa (NUC) da ke Maitama, Abuja.

ADVERTISEMENT

Ya ce haka kuma za a gudanar da zaɓen shugabannin ƙungiyar na ƙasa a washegarin ranar taron.

Dakta Imam ya ce babban baƙo na musamman shi ne Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, yayin da shugaban taron shi ne mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Sanata Kashim Shettima.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Fitiyanul Islam

Mataimakin babban sakataren ya ce babban mai ƙaddamarwa shi ne ɗan takarar shugaban ƙasa na APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, sannan babban baƙo mai jawabi shi ne Babban Limamin Masallacin Ƙasa da ke Abuja, Farfesa Ibrahim Maqari.

Ya ƙara da cewa uban taron shi ne Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, yayin da iyayen taro su ne Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi da Sheikh Shariff Ibrahim Saleh.

Sanarwar ta ce babban mai masaukin baƙi shi ne Ministan Gundumar Birnin Tarayya, Alhaji Muhammad Musa Bello, yayin da Sanata Abu Ibrahim da ɗan takarar gwamna na APC a Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, za su kasance masu taimaka masa.

Dakta Imam ya yi fatan ɗaukacin Musulmi za su yi ƙoƙari su halarci taron domin fa’idar sa.

Ita da ƙungiyar Fityanul Islam ta Nijeriya (FIN), an kafa ta ne a cikin 1962 a Kano a ƙarƙashin jagorancin Sheikh Ibrahim Inyass Al-Kaulahi (rta), kuma tun daga lokacin ta kasance mai taka muhimmiyar rawa wajen da’awar addinin Musulunci ta hanyar ɗaruruwan makarantun ta da ke cikin Nijeriya da sauran ƙasashen yankin Afrika ta Yamma.

Haka kuma ta kan yi aikin yaɗa koyarwar Annabi Muhammadu (s.a.w.), wanda ya haɗa da zaman lafiya da juna, da tsare dokokin addini da kuma neman ilimin addinin Islama.

Fitiyanul Islam
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Qatar 2022: Buhari Ya Jinjina Wa Morocco Kan Daukaka Darajar Afirka

Qatar 2022: Buhari Ya Jinjina Wa Morocco Kan Daukaka Darajar Afirka

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.