• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
PDP

Kwamitin yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, (PDPCC) ta bukaci hukumar yaki da cin hanci da rashawa (EFCC) da hukumar yaki da safaran miyagun kwayoyi (NDLEA) da su gaggauta cafke dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu kan zargin da ake masa na safaran miyagun kwayoyi da yin ruf da ciki da dukiyar jiha.

PDP din ta ce a wani taron manema labarai da suka yi a ranar Lahadi a Abuja, bayan an kama Tinubu din to a hanzarta gurfanar da shi a gaban kuliya kan wadannan zarge-zargen.

  • Naja’atu Ta Yi Murabus Daga Kwamitin Yakin Zaben Tinubu, Ta Fice Daga APC

Kakakin kwamitin yakin zaben, Mista Daniel Bwala ya bukaci NDLEA ta nemi cikakken bayani daga wajen Tinubu don ya fayyace bayanai kan dalilan da suka janyo har hukumomi a kasar Amurka suka kwace masa Dala 460,000.

Bwala, kazalika ya yi tir da wata kungiyar da ya ce Tinubu kafa, da ya ce kamar kungiyar ce ta mayakan sa-kai, sai ya nemi hukumomin tsaro da su cafke da gurfanar da duk wani da ya kasance cikin kungiyar mai suna ‘Jagaban Army’.

Sun Yi zargin cewa an kafa kungiyar ne kawai domin kawo yamutsi da firgici gabanin da yayin zabuka.

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Ya kara da cewa mambobin jam’iyyar adawa da dama su na fuskantar kalubale na barazana kashi-kashi gabanin zaben 2023.

Wani ma daga cikin masu magana da kwamitin yakin zaben PDP, Phrank Shaibu, shi ma ya zargi Tinubu har yanzu na nan tsundum cikin zargin harkarlar kwayoyi.

Kazalika kwamitin ya zargi Tinubu Wanda tsohon gwamnan Jihar Legas ne da yin sama da fadi da dukiyar jihar a lokacin da yake matsayin gwamna.

Idan za a iya tunawa a kwanakin baya ne bayanai suka karade cewa wata kotu a Amurka ta kwace wasu dalolin Amurka daga asusun Tinubu a yankin arewacin Illinois kan zargin alaka da fataucin kwayoyi.

Sai dai kuma takardun ba su bada wasu bayanai ko tabbatar da cewa anyi wa Tinubu shari’a ba, ko kuma yana da alaka da wata kungiyar fataucin kwayoyi.

Takardun sun kuma nuna cewa an yi wannan shari’a ne shekaru 30 da suka gabata.

A cewar bayanan, wannan yanayi ne ya tursasa wa Tinubu sadaukar da kudaden da yawansu ya kai dala 460,000 a daya daga cikin asusun bankunansa 10.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Next Post
Ba Zan Bar Liverpool Ba Sai Dai A Kore Ni, Cewar Klopp

Ba Zan Bar Liverpool Ba Sai Dai A Kore Ni, Cewar Klopp

LABARAI MASU NASABA

Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.