• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Koli Ta Tabbatar Lawal Dare A Matsayin Dan Takarar Gwamnan PDP A Zamfara 

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kotun Koli Ta Tabbatar Lawal Dare A Matsayin Dan Takarar Gwamnan PDP A Zamfara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun kolin ta tabbatar da Dauda Lawal Dare a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a Jihar Zamfara a zaben gwamnan jihar da za a yi ranar 11 ga watan Maris.

Alkalin kotun mai shari’a Adamu Jauro ne ya jagoranci, kwamitin alkalai biyar, ya yi watsi da karar da wani dan takarar gwamna, Dakta Ibrahim Gusau ya shigar kan zaben.

  • Sin Na Ci Gaba Da Dukufa Kan Bude Kofa Ga Ketare
  • Wani Soja Ya Hallaka Kwamandansa Ya Kuma Bindige Kansa Da Wasu Sojoji 2 A Sokoto

Ta tabbatar da abin da Mista Damian Dodo SAN, lauya ga Lawal Dare ya gabatar cewa an gabatar da wanda yake karewa bisa doka.

Jauro ya amince da hukuncin kotun daukaka kara da ta amince da zaben fidda gwani na biyu da ya samar da dan takarar.

A zaben fidda gwanin dai Lawal Dare ya samu kuri’u 442 inda ya samu nasara a kan Gusau da sauran ‘yan takara.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Jauro ya ce wata babbar kotun tarayya da ke Gusau wadda ta soke zaben fidda gwani har sau biyu ba ta da hurumi a lokacin da ta yanke hukunci kan karar da Gusau ya shigar.

Zaben fidda gwani na gwamnan PDP na farko da aka gudanar a ranar 25 ga Mayu, 2022 an kalubalanci shi a wata babbar kotun tarayya da ke Gusau kuma ta soke shi.

A hukuncin da babbar kotun ta yanke ta bayar da umarnin sake gudanar da sabon zaben fidda gwani da aka gudanar a ranar 23 ga Satumba, 2022 amma kuma kotun ta soke shi saboda wasu kurakurai.

Bai gamsu da hukuncin babbar kotun ba, Dauda Lawal-Dare, Adamu Maina-Waziri, shugaban kwamitin zaben fidda gwani; sannan Kanar Bala Mande mai ritaya ya garzaya kotun daukaka kara domin neman tazarce.

Wadanda suka amsa karar sun hada da Dakta Ibrahim Shehu-Gusau, Alhaji Wadatau Madawaki, Hafiz Nuhuche da kuma Hukumar Zabe mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC).

A cikin hukuncin da aka yanke wanda mai shari’a Abubakar Talba a madadin wasu ya karanta, kotun daukaka kara ta ce wadanda suka shigar da kara sun yi nasarar tabbatar da dukkanin wasu dalilai guda bakwai na daukaka kara da lauyoyinsu suka yi masa, kuma kotun ta yanke hukuncin ga abin da ya dace.

Talba ya yi watsi da duk wani yunkuri na farko kan cancantar karar bisa tanadin shari’a da kuma sha’awar sauraren shari’a, yana mai cewa gazawar fasaha ba za ta iya maye gurbin tanadin shari’a ba.

Ya ce alkalin babbar kotun ya yi kuskure kan takardun rangwamen da INEC ta gabatar kuma kotun ba ta ayyana lokacin sake gudanar da zabe da kuma sanarwar shiga zabe ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KotuLawal DarePDPTakarar GwamnaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Ci Gaba Da Dukufa Kan Bude Kofa Ga Ketare

Next Post

Jam’iyyar NNPP Ta Bukaci Jami’an Tsaro Su Tabbatar An Yi Sahihin Zabe A Kano

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

3 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

12 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

14 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

15 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

1 day ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

1 day ago
Next Post
Jam’iyyar NNPP Ta Bukaci Jami’an Tsaro Su Tabbatar An Yi Sahihin Zabe A Kano

Jam'iyyar NNPP Ta Bukaci Jami'an Tsaro Su Tabbatar An Yi Sahihin Zabe A Kano

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.