• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dogara Ya Mara Wa Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi Baya

by Sadiq
2 years ago
in Siyasa
0
Dogara Ya Mara Wa Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon kakakin majalisar wakilai, Yakubu Dogara, ya goya wa takarar Air Marshal Sadiqque Baba Abubakar (mai ritaya) na jam’iyyar APC a zaben gwamnan Jihar Bauchi baya.

A baya-bayan nan, Dogara ya soki tare da kin amincewa da nasarar da jam’iyyar APC ta samu tikitin takarar shugaban kasa na Musulmi da Musulmi, inda ya ce kamata ya yi jam’iyyar ta dauki Kirista daga yankin Arewacin kasar nan wanda zai mara wa Tinubu baya.

  • Babban Mai Tattara Sakamakon Zaben Atiku A Ogun Ya Sauya Sheka Zuwa APC
  • Ce-ce-kucen Al’umma Ke Ci Wa Mawakan Kannywood Tuwo A Kwarya —Jibrin Yahaya

Don haka ya shiga jirgin yakin neman zaben Atiku Abubakar na zaben shugaban kasa a 2023.

A halin yanzu, tsohon kakakin ya jagoranci tawagar yakin neman zaben Air Marshal Abubakar (mai ritaya) a wasu kananan hukumomin da suka hada da Kirfi da Alkaleri inda gwamna mai ci Bala Mohammed ya fito.

Da yake jawabi ga dimbin magoya bayansa a karamar hukumar Alkaleri ta jihar, Dogara ya bukaci jama’a da su bi tafarkin karramawa ta hanyar zaben Bala Mohammed a zaben gwamna da na ‘yan majalisar jiha da za a gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

“Mun zo ne domin mu gaya muku gaskiya cewa muna bukatar kawo sauyi a Jihar Bauchi, na zo ne domin in fadakar da ku cewa duk da cewa danku (Gwamna Bala Mohammed) yana nan amma tunda bai yi kyau ba, ya kamata mu yi, ku canza shi, ina rokon ku da ku kada kuri’u ga Air Marshal Sadiqque Abubakar ranar Asabar,” in ji shi

Ya bayyana Air Marshal Abubakar a matsayin uba, wanda zai kawo taimako ga al’ummar Jihar Bauchi.

LEADERSHIP ta tuna cewa dangantakar da ke tsakanin tsohon kakakin majalisar da Gwamna Bala Mohammed ta yi tsami, inda tsohon ya zargi shugaban da yin watsi da duk wasu yarjejeniyoyin da aka kulla kafin zaben 2019, wanda ya kawo Gwamnan kan karagar mulki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Air Marshal AbubakarBala MohammedBauchitakaraYakubu Dogara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Babban Mai Tattara Sakamakon Zaben Atiku A Ogun Ya Sauya Sheka Zuwa APC

Next Post

Mutum 14 Sun Jikkata Yayin Da Magoya PDP Da APC Suka Yi Arangama A Bauchi

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

3 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

4 days ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

6 days ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
Mutum 14 Sun Jikkata Yayin Da Magoya PDP Da APC Suka Yi Arangama A Bauchi

Mutum 14 Sun Jikkata Yayin Da Magoya PDP Da APC Suka Yi Arangama A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.