ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dogara Ya Mara Wa Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi Baya

by Sadiq
3 years ago
Dogara

Tsohon kakakin majalisar wakilai, Yakubu Dogara, ya goya wa takarar Air Marshal Sadiqque Baba Abubakar (mai ritaya) na jam’iyyar APC a zaben gwamnan Jihar Bauchi baya.

A baya-bayan nan, Dogara ya soki tare da kin amincewa da nasarar da jam’iyyar APC ta samu tikitin takarar shugaban kasa na Musulmi da Musulmi, inda ya ce kamata ya yi jam’iyyar ta dauki Kirista daga yankin Arewacin kasar nan wanda zai mara wa Tinubu baya.

  • Babban Mai Tattara Sakamakon Zaben Atiku A Ogun Ya Sauya Sheka Zuwa APC
  • Ce-ce-kucen Al’umma Ke Ci Wa Mawakan Kannywood Tuwo A Kwarya —Jibrin Yahaya

Don haka ya shiga jirgin yakin neman zaben Atiku Abubakar na zaben shugaban kasa a 2023.

ADVERTISEMENT

A halin yanzu, tsohon kakakin ya jagoranci tawagar yakin neman zaben Air Marshal Abubakar (mai ritaya) a wasu kananan hukumomin da suka hada da Kirfi da Alkaleri inda gwamna mai ci Bala Mohammed ya fito.

Da yake jawabi ga dimbin magoya bayansa a karamar hukumar Alkaleri ta jihar, Dogara ya bukaci jama’a da su bi tafarkin karramawa ta hanyar zaben Bala Mohammed a zaben gwamna da na ‘yan majalisar jiha da za a gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

“Mun zo ne domin mu gaya muku gaskiya cewa muna bukatar kawo sauyi a Jihar Bauchi, na zo ne domin in fadakar da ku cewa duk da cewa danku (Gwamna Bala Mohammed) yana nan amma tunda bai yi kyau ba, ya kamata mu yi, ku canza shi, ina rokon ku da ku kada kuri’u ga Air Marshal Sadiqque Abubakar ranar Asabar,” in ji shi

Ya bayyana Air Marshal Abubakar a matsayin uba, wanda zai kawo taimako ga al’ummar Jihar Bauchi.

LEADERSHIP ta tuna cewa dangantakar da ke tsakanin tsohon kakakin majalisar da Gwamna Bala Mohammed ta yi tsami, inda tsohon ya zargi shugaban da yin watsi da duk wasu yarjejeniyoyin da aka kulla kafin zaben 2019, wanda ya kawo Gwamnan kan karagar mulki.

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Next Post
Mutum 14 Sun Jikkata Yayin Da Magoya PDP Da APC Suka Yi Arangama A Bauchi

Mutum 14 Sun Jikkata Yayin Da Magoya PDP Da APC Suka Yi Arangama A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.