• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Ba Za A Ci Amanar Jama’a Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping: Ba Za A Ci Amanar Jama’a Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau Litinin 13 ga wata ne, aka rufe taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin NPC a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

Shugaban kasar Sin, kana babban sakataren kwamitin tsakiyar jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kuma shugaban kwamitin kolin rundunar sojan kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cikin jawabinsa yayin bikin rufe taron cewa, amincewar da jama’ar suka nuna masa, ta karfafa masa gwiwar neman samun ci gaba, wadda kuma shi ne nauyin da ke wuyansa. Xi ya kara da cewa, zai yi iyakacin kokarinsa wajen ganin ya sauke nauyin da kundin tsarin mulkin kasa ya dora masa. Zai kuma yi aiki tukutu bisa bukatun kasa, da muradun jama’a. Bugu da kari, zai sadaukar da kansa. Ba zai kuma ci amanar wakilan jama’a masu halartar taron da kuma daukacin al’ummomin kabilun kasa ba.

  • Xi Ya Sanya Hannu Kan Umarnin Shugaba Na Nada Li Qiang A Matsayin Firaministan Kasar

Xi Jinping ya jaddada cewa, za mu ci gaba da raya kasar Sin mai karfi gami da farfado da al’ummar Sinawa, kamar yadda kaka da kakaninmu suka yi a baya. Xi ya bayyana cewa, al’ummar Sinawa sun cimma gagaruman nasarori a tarihi, tare da jure wahalhalu masu yawa. Bayan kafuwar jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ta hanyar hada kan al’ummomim kabilu daban daban na kasar da kuma ba da jagora wajen yin gwagwarmaya har tsawon shekaru fiye da 100, don sake dawo mutuncinmu. Al’ummar Sinawa sun dawo da makomarsu a hannunsu. Al’ummomin Sinawa sun sake tsayawa da kafaffunsu, sun samu wadata. Yanzu suna kokarin raya kasarsu mai karfi. Ba wanda zai iya hana babban sha’anin farfado da al’ummar Sinawa. Kar a ci amanar jama’a. Wajibi ne a shugabanni su sauke nauyin da zamani da kuma tarihi ya dora musu, su ba da tasu gudummowa wajen kara azama kan raya kasar Sin mai karfi da farfado da al’ummar Sinawa, kamar yadda kaka da kakaninsu suka yi a baya.

Xi Jinping ya jaddada cewa, yayin da ake raya kasar Sin mai karfi, tilas ne a karfafa raya jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ko da yaushe a tafiyar da harkokin jam’iyyar a tsanake ba tare da kasala ba, kuma a kara yin yaki da cin hanci da karbar rashawa ba kakkautawa.

Xi Jinping ya yi nuni da cewa, za a yi kokarin zamanintar da harkokin tsaron kasa da ma rundunar sojan kasar, ta yadda rundunar sojan kasar za ta taka rawar da ta kamata wajen kare ikon mulkin kai da tsaro da moriyar ci gaban kasar.

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

Xi Jinping ya ce, ci gaban kasar Sin na haifar da alfanu ga duniya, kuma kasar Sin ba za ta iya ware kanta da sauran kasashen duniya wajen tabbatar da ci gabanta ba. Kasar Sin za ta ci gaba da bude kofarta ga duniya, da yin amfani da kasuwanni da ma albarkatu na duniya don raya kanta, tare kuma da sa kaimin ci gaban duniya baki daya.

Xi Jinping ya ci gaba da cewa, kasar Sin za ta tsaya tsayin daka wajen tabbatar da ci gaba mai inganci da kuma mai da jama’a a gaban kome, a kokarinta na raya kanta da ma farfado da al’ummar kasar, za kuma ta yi kokarin tabbatar da manufar “kasa daya amma tsarin mulki iri biyu” da dinkuwar kasar baki daya, tare da kokarin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil’adama. (Tasallah Yuan & Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sharhi: Mene Ne Ainihin Dimokuradiyya?

Next Post

Firaministan Sin Ya Nuna Cikakken Kwarin Gwiwa Kan Yanayin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Related

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara
Daga Birnin Sin

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

34 minutes ago
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva
Daga Birnin Sin

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

2 hours ago
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu
Daga Birnin Sin

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

4 hours ago
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali
Daga Birnin Sin

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

6 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

6 hours ago
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

1 day ago
Next Post
Firaministan Sin Ya Nuna Cikakken Kwarin Gwiwa Kan Yanayin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Firaministan Sin Ya Nuna Cikakken Kwarin Gwiwa Kan Yanayin Tattalin Arzikin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

May 10, 2025
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

May 10, 2025
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

May 10, 2025
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.