ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Mene Ne Ainihin Dimokuradiyya?

by CMG Hausa
3 years ago
Dimokuradiyya

“Babban nauyin da ke bisa wuyana shi ne in jagoranci mazauna kauyenmu don tabbatar da samun ci gaba da wadatar kauyen”, furucin malam Long Xianwen ke nan dan majalisar wakilan jama’ar kasar Sin.

Long Xianwen ya fito ne daga kauyen Niujiaoshan da ke yammacin lardin Hunan na kasar Sin, inda ‘yan kabilar Miao ke rayuwa. Yau shekaru sama da 10 da suka wuce, kauyen ya kasance mai talauci, inda matsakaicin kudin shigar da mazaunansa suke samu a shekara bai kai kudin Sin yuan 800 kwatankwacin dala 115 ba. Har ma akwai wakar da ‘yan kabilar Miao kan rera a wurin da ke cewa, “kada mata su auri mazan kauyen Niujiaoshan, inda ake fama da talauci, kuma daga cikin maza 10, 9 sun kasance gwagare.”

  • Jami’in Afirka ta kudu: Tsarin Demokuradiyya Na Sin Ya Mayar Da Hankali Kan Jama’ar Kasar

Amma yanzu kauyen ya samu matukar gyaran fuska, inda a karkashin jagorancin Long Xianwen, mazauna kauyen suka yi amfani da albarkatun da suke da su, suka fara noman bishiyoyin ganyen shayi a duwatsu, baya ga bunkasa harkokin yawon shakatawa, matakin da ya sa cikin shekaru sama da 10, aka fitar da kauyen daga kangin talauci, inda matsakaicin kudin shigar mazaunasa ya karu da sau 18. A matsayinsa na jagoran kauyen, Long Xianwen ma ya samu goyon baya sosai daga mazauna kauyen, har ma an zabe shi a matsayin dan majalisar wakilan jama’ar kasar Sin har sau biyu a jere tun daga shekarar 2018. A matsayinsa na dan majalisar, Long Xianwen kusan ya tafi kowane sashe na karkarar yankin yammacin lardin Hunan, kuma ta hanyar ziyartar al’umma da sauraron ra’ayoyinsu da gudanar da bincike, ya fahimci ainihin matsalolin da suke fuskanta, tare da bayyana ra’ayoyi da ma shawarwarinsu a wajen taron majalisar wakilan jama’ar kasar, ta yadda gwamnatin kasar za ta samu damar fahimtar matsalolin da al’ummarta ke fuskanta.

ADVERTISEMENT

A hakika, Long Xianwen na daga cikin ‘yan majalisar wakilan jama’ar kasar Sin karo na 14 da gaba dayansu suka kai 2977, wadanda suke gudanar da aikinsu don bauta wa al’ummar kasar. A kasar Sin, ban da ‘yan majalisar wakilan jama’a a mataki na kasa, akwai kuma ‘yan majalisar wakilan jama’a a matsayin larduna da birane da gundumomi da garuruwa, wadanda suke wakiltar al’umma ‘yan kabilu daban daban da ma mabambantan yankuna da sana’o’i. ‘Yan majalisar a matakai daban daban sun bayyana ra’ayoyin al’umma da sa ido a kan yadda gwamnati ke tafiyar da harkoki da kuma sa kaimin warware matsalolin da al’umma ke fuskanta a turbar dimokuradiyyar al’umma baki daya.

A ganin gwamnatin kasar Sin da al’ummarta, dimokuradiyya ba ado ba ne, hanya ce ta warware matsalolin da al’umma ke fuskanta, kuma dimokuradiyya na da mabambantan salo a kasashe daban daban bisa yanayin da suke ciki. Kasancewar kasar Sin kasa mai fadi wadda ke da mafi yawan al’umma a duniya, jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ta hada gwiwa da sauran jam’iyyun siyasa na kasar, suka gano hanyar dimokuradiyyar da ta dace da yanayin da take ciki.

LABARAI MASU NASABA

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

Jama’ar wata kasa ne suke da ‘yancin tabbatar da ko kasar na kan tafarkin dimokuradiyya ko a’a. Binciken sauraron ra’ayoyin al’umma ya shaida cewa, cikin ‘yan shekarun baya, gwamnatin kasar Sin ta kiyaye sama da kaso 90% na amincewar da al’ummarta suka nuna mata, lamarin da ya shaida ingancin dimokuradiyya a kasar Sin.(Mai Zane:Mustapha Bulama)

Dimokuradiyya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar
Daga Birnin Sin

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

June 17, 2026
Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

June 17, 2026
Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku
Daga Birnin Sin

Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

June 17, 2026
Next Post
Xi Jinping: Ba Za A Ci Amanar Jama’a Ba

Xi Jinping: Ba Za A Ci Amanar Jama’a Ba

LABARAI MASU NASABA

’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Sace Limami Da Wasu Mutane 7 A Filato

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

June 18, 2026
Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

June 18, 2026
Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

June 17, 2026
Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

June 17, 2026
Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

June 17, 2026
Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

June 17, 2026
Sin Na Gaggauta Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Kasa Da Kasa

Sin Na Gaggauta Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Kasa Da Kasa

June 17, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Takardar Bayani Game Da Inganta Tsarin Jagorancin Harkokin Duniya

Kasar Sin Ta Gabatar Da Takardar Bayani Game Da Inganta Tsarin Jagorancin Harkokin Duniya

June 17, 2026
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Ceto Manoma 7 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Sakkwato, Sun Ƙwato Babura

June 17, 2026
Liu Guozhong Ya Halarci Taron Koli Kan Yadda Kasashen Afirka Za Su Fuskanci Cutar Ebola

Liu Guozhong Ya Halarci Taron Koli Kan Yadda Kasashen Afirka Za Su Fuskanci Cutar Ebola

June 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.