• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta 10: Gwamnoni 25 Sun Mara Wa Akpabio Da Barau Baya

by Sadiq
2 years ago
Majalisa

Gabanin shiga zaben Majalisar Dokokin kasar nan karo na 10 a ranar Talata 13 ga watan Yuni 2023, gwamnonin jihohi akalla 25 ne suka zabi Sanata Godswill Obong Akpabio, da Sanata Jibrin Barau a matsayin shugaban majalisar dattawa da mataimakin shugaban majalisar dattawa na majalisa ta 10.

Gwamnonin sun hada kai da zababbun Sanatoci na manyan jam’iyyu uku: APC, PDP da kuma jam’iyyar LP domin mara wa ‘yan takarar baya.

  • Sin Ta Bude Ofishin Jakadanci S Kasar Honduras.
  • Xi Jinping: Ana Kokarin Yaki Da Yaduwar Hamada A Sin Don Bude Sabon Babi

Daga cikin gwamnonin guda 25 da ke goyon bayan Akpabio sun hada da Gwamnonin Kwara, Nasarawa, Benue, Ogun, Oyo, Legas, Ekiti, Osun, Kogi, Ribas, Kuros Riba, Kaduna, Borno, Ebonyi da kuma Ondo.

Gwamnonin, wadanda akasarinsu na Jihohin da ke karkashin Jam’iyyar APC ne, sun ci gaba da cewa, sun yi kakkausar suka wajen amincewa da shawarar da Kwamitin Ayyuka na Kasa (NWC) na jam’iyya mai mulki ya dauka.

Gwamnonin sun kara da cewa jam’iyyar APC ta yanke shawara mafi inganci da za ta inganta zaman lafiya a hukumomi da kuma gudanar da harkokin majalisa cikin lumana a majalisa ta kasa ta 10 nan da shekara hudu masu zuwa.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Musamman a lokacin da Akpabio ya ziyarci Gwamna Yahaya Bello a Jihar Kogi, gwamnan ya bayyana burin Akpabio da Barau na lashe kujerun shugaban majalisar dattawa da mataimaki a majalisa ta 10.

Ya kuma bayyana cewa Akpabio, tsohon ministan harkokin Neja-Delta, shi ne abin koyinsa, inda ya kara da cewa salon mulkin Sanatan da ba a saba gani ba a matsayinsa na gwamnan Jihar Akwa Ibom, ya sa ya so ya zama kamar tsohon gwamnan.

Gwamnan Kogi ya ce zai yi kokarin ganin an samu kwanciyar hankali a fadar shugaban kasa Bola Tinubu.

Har ila yau, gwamnan Jihar Ekiti, Biodun Oyebanji, ya ce zababbun sanatoci da sauran masu ruwa da tsaki a jihar ne ke goyon bayan takarar Sanata Akpabio don ya gaji Ahmad Lawan a matsayin shugaban majalisar dattawa.

Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya kuma bayyana cewa gwamnonin APC na Arewa cewa sun kuduri aniyar mara wa shugaba Bola Tinubu baya na zaben shugabannin majalisar dokokin kasar nan.

Gwamna Babajide Sanwo a Jihar Legas ya ce yana fatan Majalisar ta 10 za ta kasance ne kan “Sarfafa sabbin dokoki” don inganta abubuwan da aka riga aka yi a Majalisar ta tara.

Ya bayyana kungiyar zababbun Sanatoci a fadin jam’iyyar a matsayin “kungiyar da ta yi aiki sosai”.

Har ila yau, wata majiya ta kusa da Gwamnonin APC ta yi nuni da cewa, suna sa ran ganin an samu zaman lafiya, kwanciyar hankali a zauren majalisar ta 10.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Kama Aiki A Fadar Shugaban Kasa

Kotu Ta Bukaci Masu Kalubalantar Nasarar Tinubu Su Biya Miliyan 10 Kowannensu

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.