• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Zabarmawan Nijeriya Ta Nesanta Kanta Daga Shugabancin Alhaji Aliyu Abubakar

by Bello Hamza
2 years ago
in Rahotonni
0
Kungiyar Zabarmawan Nijeriya Ta Nesanta Kanta Daga Shugabancin Alhaji Aliyu Abubakar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan kungiyar Zabarmawan Nijeriya a karkashin jagorancin Sarkin Zabarmawan Nijeriya, Alhaji Ibrahim Mahmud Tsamiya, sun nesanta kansu daga shugabancin wani mutum mai suna Alhaji Aliyu Abubakar wanda Mai Martaba Sarkin Sasha Alhaji Haruna Mai Yasin, Sardaunan Yamma ya nada a fadarsa dake Ibadan a ranar 9 ga watan Yulin 2023.

kungiyar ta ce sam ba su amince ba da wannan nadin. Domin ba za su amince da shugabancin wanda ba Zabarmawa ne suka amince da shi ba. A don haka sun ce nadin da aka yi wa Alhaji Aliyu Abubakar ba su san da shi ba, kuma shugabansu a Nijeriya shi ne Alhaji Ibrahim Mahmud Tsamiya kuma gare shi suka yi mubaya’arsu.

  • Gwamna Uba Sani Ya Yi Sabbin Nade-naden Mukamai A Jihar Kaduna

Zabarmawan na Nijeriya sun bayyana hakan ne a taron da suka kira a ranar Asabar 15 ga watan nan da ake ciki a Fadar Sarkin Zabarmawan Ikeja da ke Shodipe Agege domin tattaunawa a kan nadin Sarkin Zabarmawa na jihohin kudu goma sha bakwai da Sarkin Sasa ya nada kuma suke nesanta kansu ga shi.

Zabarmawan sun nuna rashin amincewarsu a kan wannan nadin, inda suka tabbatar da cewa ba za su bari wasu su raba kawukansu ba.

Dakta Lawal Sani Kasgada, Sakataren kasa na kungiyar Zabarmawa zallah ta Nijeriya ya ce sun kira taron ne domin jaddada mubaya’arsu ga jagorancinsa na Sarkin Zabarmawan Nijeriya; “Wadanda Zabarmawa zallah suka zaba ya shugabance su a matsayin Sarkin Zabarmawan Nijeriya. Duk Zabarmawan da ke Nijeriya suna mubaya’a ga shi. A bayan haka kuma muna kara nesantar da kanmu a kan duk wani Basarake da za a ce a nan Kudu wani Bahaushe ya nada. Duk Basarake ko Bazarmane Bahaushe ya nada da sunan Zabarmawa mu ba za mu aminta ba, ba ma tare da shi”, ya jaddada.

Labarai Masu Nasaba

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

Lawal ya ci gaba da cewa Zabarmawa yare ne masu ‘yanci, inda ya ce; “a don haka Bazamarme ne zai nada mana Bazamarme. Duk wani wanda yake son sarauta a jihohin Kudu, to ya zo fadar mai girma Sarkin Zabarmawan Nijeriya a nada shi. Idan kuma ya bar wannan ya je wurin wani Sarki wanda ba Bazamarme ba, wannan yanayi ne a karon kansa. Duk wani wanda ya yi hulda da shi a matsayin Basaraken Zabarmawa da ke kudu, to ya yi wannan ne a gaban kansa.

Zabarmawa ba su da alaka da wannan, ba su da alaka da shi. Kuma ba su amince da shi ba, a don haka mubaya’armu yana ga Sarkin Zabarmawan Nijeriya da duk kuma wanda shi ya nada idan dai a Kudancin Nijeriya ne; wato jihohi goma sha bakwai na jihohin Nijeriya.

“Kuma wannan maganar da nake yi ina yin shi ne a madadin dukkanin Zabarmawan da ke Nijeriya da Sarakunan kudun Zabarmawa wadanda ke Nijeriya tun daga Fatakwal da ke jihar Ribas har zuwa Legas, Ogun, Osun, Imo, Ondo, Kuros Ribas, Bayelsa, duk dai jihohin nan guda goma sha bakwai”, ya nusasshe.

Ya yi kira ga Zabarmawan Nijeriya da su wanzar da zaman lafiya. Kuma ka da su dauki doka a hannu, inda ya aara da cewa; “A don haka kuma bayan haka muna kira ga Zabarmawa da su zauna lafiya, duk Zabarmawa daya ne. A hada kai, ka da a dauki doka a hannu. Zaman lafiya shi ne abu ingantacce. Abin da zaman lafiya bai kawo ba, tashin hankali ba zai kawo shi ba.

Musamman wannan kasa ta mu da take cikin rigingimun barazanar tsaro. Mu ba hukumomin tsaro damar su, mu ba su goyon baya. Ka da kowa ya dauki doka a hannunsa. Bazamarme dan uwan Bazamarme ne. Bazamarme dan uwan Nijeriya ne gaba daya a matsayinmu na al’umma daya, kasa daya, wanda aka raba ba”.

Alhaji Yahaya, dan majalisar Sarkin Zabarmawan Ikorodu, ya nemi a zauna lafiya tare da yin biyyaya ga masarautar Zabarmawa da aka sani, wato karkashin jagorancin Sarkin Zabarmawan Nijeriya wato Alhaji Ibrahim Tsamiya. Taron ya samu halartar dimbin jama’a da suka hada da Sarakunan gargajiya, ‘yan kasuwa da matasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Gana Da Tsohon Shugaban jam’iyyar APC Na Kasa Da Sakatarensa

Next Post

An Kaddamar Da Gasar Fasaha Ta Matasan Afirka Da Sin Ta Dauki Nauyin Shiryawa A Kenya

Related

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

1 day ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

3 days ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

5 days ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

2 weeks ago
Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu
Rahotonni

Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

2 weeks ago
Next Post
An Kaddamar Da Gasar Fasaha Ta Matasan Afirka Da Sin Ta Dauki Nauyin Shiryawa A Kenya

An Kaddamar Da Gasar Fasaha Ta Matasan Afirka Da Sin Ta Dauki Nauyin Shiryawa A Kenya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

September 9, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

September 9, 2025
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.