• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Zabarmawan Nijeriya Ta Nesanta Kanta Daga Shugabancin Alhaji Aliyu Abubakar

by Bello Hamza
2 years ago
in Rahotonni
0
Kungiyar Zabarmawan Nijeriya Ta Nesanta Kanta Daga Shugabancin Alhaji Aliyu Abubakar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan kungiyar Zabarmawan Nijeriya a karkashin jagorancin Sarkin Zabarmawan Nijeriya, Alhaji Ibrahim Mahmud Tsamiya, sun nesanta kansu daga shugabancin wani mutum mai suna Alhaji Aliyu Abubakar wanda Mai Martaba Sarkin Sasha Alhaji Haruna Mai Yasin, Sardaunan Yamma ya nada a fadarsa dake Ibadan a ranar 9 ga watan Yulin 2023.

kungiyar ta ce sam ba su amince ba da wannan nadin. Domin ba za su amince da shugabancin wanda ba Zabarmawa ne suka amince da shi ba. A don haka sun ce nadin da aka yi wa Alhaji Aliyu Abubakar ba su san da shi ba, kuma shugabansu a Nijeriya shi ne Alhaji Ibrahim Mahmud Tsamiya kuma gare shi suka yi mubaya’arsu.

  • Gwamna Uba Sani Ya Yi Sabbin Nade-naden Mukamai A Jihar Kaduna

Zabarmawan na Nijeriya sun bayyana hakan ne a taron da suka kira a ranar Asabar 15 ga watan nan da ake ciki a Fadar Sarkin Zabarmawan Ikeja da ke Shodipe Agege domin tattaunawa a kan nadin Sarkin Zabarmawa na jihohin kudu goma sha bakwai da Sarkin Sasa ya nada kuma suke nesanta kansu ga shi.

Zabarmawan sun nuna rashin amincewarsu a kan wannan nadin, inda suka tabbatar da cewa ba za su bari wasu su raba kawukansu ba.

Dakta Lawal Sani Kasgada, Sakataren kasa na kungiyar Zabarmawa zallah ta Nijeriya ya ce sun kira taron ne domin jaddada mubaya’arsu ga jagorancinsa na Sarkin Zabarmawan Nijeriya; “Wadanda Zabarmawa zallah suka zaba ya shugabance su a matsayin Sarkin Zabarmawan Nijeriya. Duk Zabarmawan da ke Nijeriya suna mubaya’a ga shi. A bayan haka kuma muna kara nesantar da kanmu a kan duk wani Basarake da za a ce a nan Kudu wani Bahaushe ya nada. Duk Basarake ko Bazarmane Bahaushe ya nada da sunan Zabarmawa mu ba za mu aminta ba, ba ma tare da shi”, ya jaddada.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Lawal ya ci gaba da cewa Zabarmawa yare ne masu ‘yanci, inda ya ce; “a don haka Bazamarme ne zai nada mana Bazamarme. Duk wani wanda yake son sarauta a jihohin Kudu, to ya zo fadar mai girma Sarkin Zabarmawan Nijeriya a nada shi. Idan kuma ya bar wannan ya je wurin wani Sarki wanda ba Bazamarme ba, wannan yanayi ne a karon kansa. Duk wani wanda ya yi hulda da shi a matsayin Basaraken Zabarmawa da ke kudu, to ya yi wannan ne a gaban kansa.

Zabarmawa ba su da alaka da wannan, ba su da alaka da shi. Kuma ba su amince da shi ba, a don haka mubaya’armu yana ga Sarkin Zabarmawan Nijeriya da duk kuma wanda shi ya nada idan dai a Kudancin Nijeriya ne; wato jihohi goma sha bakwai na jihohin Nijeriya.

“Kuma wannan maganar da nake yi ina yin shi ne a madadin dukkanin Zabarmawan da ke Nijeriya da Sarakunan kudun Zabarmawa wadanda ke Nijeriya tun daga Fatakwal da ke jihar Ribas har zuwa Legas, Ogun, Osun, Imo, Ondo, Kuros Ribas, Bayelsa, duk dai jihohin nan guda goma sha bakwai”, ya nusasshe.

Ya yi kira ga Zabarmawan Nijeriya da su wanzar da zaman lafiya. Kuma ka da su dauki doka a hannu, inda ya aara da cewa; “A don haka kuma bayan haka muna kira ga Zabarmawa da su zauna lafiya, duk Zabarmawa daya ne. A hada kai, ka da a dauki doka a hannu. Zaman lafiya shi ne abu ingantacce. Abin da zaman lafiya bai kawo ba, tashin hankali ba zai kawo shi ba.

Musamman wannan kasa ta mu da take cikin rigingimun barazanar tsaro. Mu ba hukumomin tsaro damar su, mu ba su goyon baya. Ka da kowa ya dauki doka a hannunsa. Bazamarme dan uwan Bazamarme ne. Bazamarme dan uwan Nijeriya ne gaba daya a matsayinmu na al’umma daya, kasa daya, wanda aka raba ba”.

Alhaji Yahaya, dan majalisar Sarkin Zabarmawan Ikorodu, ya nemi a zauna lafiya tare da yin biyyaya ga masarautar Zabarmawa da aka sani, wato karkashin jagorancin Sarkin Zabarmawan Nijeriya wato Alhaji Ibrahim Tsamiya. Taron ya samu halartar dimbin jama’a da suka hada da Sarakunan gargajiya, ‘yan kasuwa da matasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Gana Da Tsohon Shugaban jam’iyyar APC Na Kasa Da Sakatarensa

Next Post

An Kaddamar Da Gasar Fasaha Ta Matasan Afirka Da Sin Ta Dauki Nauyin Shiryawa A Kenya

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
Zabarmawan Nijeriya
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

4 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

4 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
An Kaddamar Da Gasar Fasaha Ta Matasan Afirka Da Sin Ta Dauki Nauyin Shiryawa A Kenya

An Kaddamar Da Gasar Fasaha Ta Matasan Afirka Da Sin Ta Dauki Nauyin Shiryawa A Kenya

LABARAI MASU NASABA

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.