ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Zabarmawan Nijeriya Ta Nesanta Kanta Daga Shugabancin Alhaji Aliyu Abubakar

by Bello Hamza
3 years ago
Zabarmawan Nijeriya

‘Yan kungiyar Zabarmawan Nijeriya a karkashin jagorancin Sarkin Zabarmawan Nijeriya, Alhaji Ibrahim Mahmud Tsamiya, sun nesanta kansu daga shugabancin wani mutum mai suna Alhaji Aliyu Abubakar wanda Mai Martaba Sarkin Sasha Alhaji Haruna Mai Yasin, Sardaunan Yamma ya nada a fadarsa dake Ibadan a ranar 9 ga watan Yulin 2023.

kungiyar ta ce sam ba su amince ba da wannan nadin. Domin ba za su amince da shugabancin wanda ba Zabarmawa ne suka amince da shi ba. A don haka sun ce nadin da aka yi wa Alhaji Aliyu Abubakar ba su san da shi ba, kuma shugabansu a Nijeriya shi ne Alhaji Ibrahim Mahmud Tsamiya kuma gare shi suka yi mubaya’arsu.

  • Gwamna Uba Sani Ya Yi Sabbin Nade-naden Mukamai A Jihar Kaduna

Zabarmawan na Nijeriya sun bayyana hakan ne a taron da suka kira a ranar Asabar 15 ga watan nan da ake ciki a Fadar Sarkin Zabarmawan Ikeja da ke Shodipe Agege domin tattaunawa a kan nadin Sarkin Zabarmawa na jihohin kudu goma sha bakwai da Sarkin Sasa ya nada kuma suke nesanta kansu ga shi.

ADVERTISEMENT

Zabarmawan sun nuna rashin amincewarsu a kan wannan nadin, inda suka tabbatar da cewa ba za su bari wasu su raba kawukansu ba.

Dakta Lawal Sani Kasgada, Sakataren kasa na kungiyar Zabarmawa zallah ta Nijeriya ya ce sun kira taron ne domin jaddada mubaya’arsu ga jagorancinsa na Sarkin Zabarmawan Nijeriya; “Wadanda Zabarmawa zallah suka zaba ya shugabance su a matsayin Sarkin Zabarmawan Nijeriya. Duk Zabarmawan da ke Nijeriya suna mubaya’a ga shi. A bayan haka kuma muna kara nesantar da kanmu a kan duk wani Basarake da za a ce a nan Kudu wani Bahaushe ya nada. Duk Basarake ko Bazarmane Bahaushe ya nada da sunan Zabarmawa mu ba za mu aminta ba, ba ma tare da shi”, ya jaddada.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Lawal ya ci gaba da cewa Zabarmawa yare ne masu ‘yanci, inda ya ce; “a don haka Bazamarme ne zai nada mana Bazamarme. Duk wani wanda yake son sarauta a jihohin Kudu, to ya zo fadar mai girma Sarkin Zabarmawan Nijeriya a nada shi. Idan kuma ya bar wannan ya je wurin wani Sarki wanda ba Bazamarme ba, wannan yanayi ne a karon kansa. Duk wani wanda ya yi hulda da shi a matsayin Basaraken Zabarmawa da ke kudu, to ya yi wannan ne a gaban kansa.

Zabarmawa ba su da alaka da wannan, ba su da alaka da shi. Kuma ba su amince da shi ba, a don haka mubaya’armu yana ga Sarkin Zabarmawan Nijeriya da duk kuma wanda shi ya nada idan dai a Kudancin Nijeriya ne; wato jihohi goma sha bakwai na jihohin Nijeriya.

“Kuma wannan maganar da nake yi ina yin shi ne a madadin dukkanin Zabarmawan da ke Nijeriya da Sarakunan kudun Zabarmawa wadanda ke Nijeriya tun daga Fatakwal da ke jihar Ribas har zuwa Legas, Ogun, Osun, Imo, Ondo, Kuros Ribas, Bayelsa, duk dai jihohin nan guda goma sha bakwai”, ya nusasshe.

Ya yi kira ga Zabarmawan Nijeriya da su wanzar da zaman lafiya. Kuma ka da su dauki doka a hannu, inda ya aara da cewa; “A don haka kuma bayan haka muna kira ga Zabarmawa da su zauna lafiya, duk Zabarmawa daya ne. A hada kai, ka da a dauki doka a hannu. Zaman lafiya shi ne abu ingantacce. Abin da zaman lafiya bai kawo ba, tashin hankali ba zai kawo shi ba.

Musamman wannan kasa ta mu da take cikin rigingimun barazanar tsaro. Mu ba hukumomin tsaro damar su, mu ba su goyon baya. Ka da kowa ya dauki doka a hannunsa. Bazamarme dan uwan Bazamarme ne. Bazamarme dan uwan Nijeriya ne gaba daya a matsayinmu na al’umma daya, kasa daya, wanda aka raba ba”.

Alhaji Yahaya, dan majalisar Sarkin Zabarmawan Ikorodu, ya nemi a zauna lafiya tare da yin biyyaya ga masarautar Zabarmawa da aka sani, wato karkashin jagorancin Sarkin Zabarmawan Nijeriya wato Alhaji Ibrahim Tsamiya. Taron ya samu halartar dimbin jama’a da suka hada da Sarakunan gargajiya, ‘yan kasuwa da matasa.

Zabarmawan Nijeriya
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
An Kaddamar Da Gasar Fasaha Ta Matasan Afirka Da Sin Ta Dauki Nauyin Shiryawa A Kenya

An Kaddamar Da Gasar Fasaha Ta Matasan Afirka Da Sin Ta Dauki Nauyin Shiryawa A Kenya

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.