ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Zabarmawan Nijeriya Ta Nesanta Kanta Daga Shugabancin Alhaji Aliyu Abubakar

by Bello Hamza
3 years ago
Zabarmawan Nijeriya

‘Yan kungiyar Zabarmawan Nijeriya a karkashin jagorancin Sarkin Zabarmawan Nijeriya, Alhaji Ibrahim Mahmud Tsamiya, sun nesanta kansu daga shugabancin wani mutum mai suna Alhaji Aliyu Abubakar wanda Mai Martaba Sarkin Sasha Alhaji Haruna Mai Yasin, Sardaunan Yamma ya nada a fadarsa dake Ibadan a ranar 9 ga watan Yulin 2023.

kungiyar ta ce sam ba su amince ba da wannan nadin. Domin ba za su amince da shugabancin wanda ba Zabarmawa ne suka amince da shi ba. A don haka sun ce nadin da aka yi wa Alhaji Aliyu Abubakar ba su san da shi ba, kuma shugabansu a Nijeriya shi ne Alhaji Ibrahim Mahmud Tsamiya kuma gare shi suka yi mubaya’arsu.

  • Gwamna Uba Sani Ya Yi Sabbin Nade-naden Mukamai A Jihar Kaduna

Zabarmawan na Nijeriya sun bayyana hakan ne a taron da suka kira a ranar Asabar 15 ga watan nan da ake ciki a Fadar Sarkin Zabarmawan Ikeja da ke Shodipe Agege domin tattaunawa a kan nadin Sarkin Zabarmawa na jihohin kudu goma sha bakwai da Sarkin Sasa ya nada kuma suke nesanta kansu ga shi.

ADVERTISEMENT

Zabarmawan sun nuna rashin amincewarsu a kan wannan nadin, inda suka tabbatar da cewa ba za su bari wasu su raba kawukansu ba.

Dakta Lawal Sani Kasgada, Sakataren kasa na kungiyar Zabarmawa zallah ta Nijeriya ya ce sun kira taron ne domin jaddada mubaya’arsu ga jagorancinsa na Sarkin Zabarmawan Nijeriya; “Wadanda Zabarmawa zallah suka zaba ya shugabance su a matsayin Sarkin Zabarmawan Nijeriya. Duk Zabarmawan da ke Nijeriya suna mubaya’a ga shi. A bayan haka kuma muna kara nesantar da kanmu a kan duk wani Basarake da za a ce a nan Kudu wani Bahaushe ya nada. Duk Basarake ko Bazarmane Bahaushe ya nada da sunan Zabarmawa mu ba za mu aminta ba, ba ma tare da shi”, ya jaddada.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Lawal ya ci gaba da cewa Zabarmawa yare ne masu ‘yanci, inda ya ce; “a don haka Bazamarme ne zai nada mana Bazamarme. Duk wani wanda yake son sarauta a jihohin Kudu, to ya zo fadar mai girma Sarkin Zabarmawan Nijeriya a nada shi. Idan kuma ya bar wannan ya je wurin wani Sarki wanda ba Bazamarme ba, wannan yanayi ne a karon kansa. Duk wani wanda ya yi hulda da shi a matsayin Basaraken Zabarmawa da ke kudu, to ya yi wannan ne a gaban kansa.

Zabarmawa ba su da alaka da wannan, ba su da alaka da shi. Kuma ba su amince da shi ba, a don haka mubaya’armu yana ga Sarkin Zabarmawan Nijeriya da duk kuma wanda shi ya nada idan dai a Kudancin Nijeriya ne; wato jihohi goma sha bakwai na jihohin Nijeriya.

“Kuma wannan maganar da nake yi ina yin shi ne a madadin dukkanin Zabarmawan da ke Nijeriya da Sarakunan kudun Zabarmawa wadanda ke Nijeriya tun daga Fatakwal da ke jihar Ribas har zuwa Legas, Ogun, Osun, Imo, Ondo, Kuros Ribas, Bayelsa, duk dai jihohin nan guda goma sha bakwai”, ya nusasshe.

Ya yi kira ga Zabarmawan Nijeriya da su wanzar da zaman lafiya. Kuma ka da su dauki doka a hannu, inda ya aara da cewa; “A don haka kuma bayan haka muna kira ga Zabarmawa da su zauna lafiya, duk Zabarmawa daya ne. A hada kai, ka da a dauki doka a hannu. Zaman lafiya shi ne abu ingantacce. Abin da zaman lafiya bai kawo ba, tashin hankali ba zai kawo shi ba.

Musamman wannan kasa ta mu da take cikin rigingimun barazanar tsaro. Mu ba hukumomin tsaro damar su, mu ba su goyon baya. Ka da kowa ya dauki doka a hannunsa. Bazamarme dan uwan Bazamarme ne. Bazamarme dan uwan Nijeriya ne gaba daya a matsayinmu na al’umma daya, kasa daya, wanda aka raba ba”.

Alhaji Yahaya, dan majalisar Sarkin Zabarmawan Ikorodu, ya nemi a zauna lafiya tare da yin biyyaya ga masarautar Zabarmawa da aka sani, wato karkashin jagorancin Sarkin Zabarmawan Nijeriya wato Alhaji Ibrahim Tsamiya. Taron ya samu halartar dimbin jama’a da suka hada da Sarakunan gargajiya, ‘yan kasuwa da matasa.

Zabarmawan Nijeriya
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
An Kaddamar Da Gasar Fasaha Ta Matasan Afirka Da Sin Ta Dauki Nauyin Shiryawa A Kenya

An Kaddamar Da Gasar Fasaha Ta Matasan Afirka Da Sin Ta Dauki Nauyin Shiryawa A Kenya

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.